ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ba Da Belin El-Rufai Kan Naira Miliyan 100

by Rabi'u Ali Indabawa
2 weeks ago

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da belin tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.

Kotun ta bayar da belin ne kan kuɗi Naira miliyan 100 tare da mutum ɗaya da zai tsaya masa da makamancin wannan adadi.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta gindaya tsauraran sharuɗa kan belin, inda ta ce wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance mazaunin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya ajiye asalin takardar mallakar gida (Certificate of Occupancy) na wata kadara a gaban kotu.

ADVERTISEMENT

Kotun ta kuma umurci wanda zai tsaya masa da ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai mataki na 17 ko sama da haka, tare da gabatar da shaidar albashi na aƙalla watanni uku.

Bugu da ƙari, dole ne wanda zai tsaya masa ya gabatar da takardar shaidar hali ta kuɗi, ya rattaba hannu kan yarjejeniyar beli, sannan ya bayar da hoton fasfo na baya-bayan nan tare da wasiƙar tabbatarwa daga ma’aikatarsa da takardar biyan haraji ta watanni shida da suka gabata.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Kotun ta kuma umurci El-Rufai da ya miƙa dukkan ingantattun fasfo na ƙasashen waje da yake da su.

Mai shari’a Abdulmalik ta kuma umurce shi da ya riƙa zuwa hedikwatar DSS duk ranar Juma’a ta ƙarshe a kowane wata da ƙarfe 10 na safe domin sanya hannu a rajistar halarta har sai an kammala shari’ar.

Kotun ta yi gargaɗin cewa duk wani karya waɗannan sharuɗa zai janyo soke belin kai tsaye.

Jaridar Daily Trust ta rawaito yadda aka gurfanar da tsohon gwamnan bisa zargin saƙa na’urar sauraren wayar mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

An kawo tsohon gwamnan harabar kotun da misalin ƙarfe 8:55 na safe ranar Litinin tare da jami’an tsaron farin kaya masu tsaurin fuska, waɗanda suka killace harabar kotun.

An hana ƴan jarida, ma’aikata da sauran masu amfani da harabar kotun shiga nan take bayan kawo tsohon gwamnan, lamarin da ya haddasa ɗan zanga-zanga na ɗan lokaci.

Jagoran zanga-zangar, ɗan gwagwarmaya kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, ya ce kotu wuri ne na jama’a wanda bai kamata a hana duk wani ɗan Nijeriya mai sha’awar sauraren shari’a shiga ba.

Da yake magana da Daily Trust ba tare da bayyana sunansa ba, wani ma’aikacin ICPC ya bayyana cewa jami’an DSS sun isa ofishin hukumar tun ƙarfe 7:00 na safe domin ɗaukar wanda ake tuhuma zuwa kotu.

“Eh, shari’ar da ake yi yanzu ba tamu ba ce. Su jami’an DSS sun zo ɗaukar sa da misalin ƙarfe 7:00 na safe domin gurfanar da shi a kotu,” in ji majiyar.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sarki Aminu Ya Sanar Da Ƴansanda, DSS Zai Yi Hawan Sallah

Sarki Aminu Ya Sanar Da Ƴansanda, DSS Zai Yi Hawan Sallah

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.