ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Na Ci Gaba Da Kumfar Baki Kan Nasarar Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Ga dukkan alamu, masu adawa da ayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben 2023 na ci gaba da matsa kaimi da tayar da jijiyoyin wuya da kumfar baki musamman game da rantsar da shi a ranar 29 ga Mayun 2023.

Mafi yawancin ‘yan adawa wadanda ba su ji dadin sakamakon zaben ba, sun bukaci kar a rantsar da Tinubu a matsayin shugaban kasa har sai kotu ta kammala shari’ar da ke gabanta, saboda a cewarsu, zaben na cike da magudi.

  • Waiwaye Game Da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida Ta Duniya
  • Montana Ta Zama Jihar Amurka Ta Farko Da Ta Haramta TikTok

Haka kuma sun bukaci a kafa gwamnatin rikon kwarya idan wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shude.

ADVERTISEMENT

Masu shigar da karar sun kuma bukaci a fitar da sanarwar tsawaita wa’adin mulkin shugaban kasa, Muhammadu Buhari har sai an tantance wanda zai gaje shi kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

A yayin zaman da aka yi a ranar Litinin, lauyan wadanda suka shigar da kara, Chuks Nwachukwu, ya shaida wa kotun cewa sun shigar da karar ne domin kotun daukaka kara ta hana duk wani tsarin mika mulki.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Da yake zantawa da manema labarai bayan zaman kotun, Nwachukwu ya bayyana cewa zababben shugaban kasar bai cika dukkan abubuwan da ake bukata kafin zama shugaban kasa.

Ya ce hujjar cewa shugabannin da suka shude sun fuskanci koke-koke bayan an rantsar da su kan karagar mulki.

A cewarsa, shuwagabannin da suka shude sun cika dukkan abubuwan da ake bukata kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

Ya kara da cewa, “Suna bukatar dukkan akwatunan da takarda zabe da aka yi amfani da su lokacin zabe. Amma kundin tsarin mulkin kasar bai dauki Tinubu a matsayin wanda ya dace ya zama shugaban kasa ba, saboda bai cika sharudda ba.”

Ya ce shi bai damu da masu ra’ayin cewa za a yi tazarce idan ba a rantsar da Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu, saboda tsarin mulki ya bai wa shugaban kasa mai ci damar kula da al’amuran kasa har sai wanda ya cancanta ya karbi mulki.

Nwachukwu ya ce, “Muna tabbatar da cewa babu wanda zai fahimci manufarmu. Masu shigar da kara na zaben suna ta kokawa a tsakaninsu kan wanda ya kamata ya yi nasara. Ba mu sha’awa a kan wanda zai yi nasara.

 “Abin da muke sha’awar shi ne duk wanda za a rantsar da shi ya samu kashi 25 cikin 100 na kuri’un da aka jefa a jihoji ciki har da Abuja idan kuma ba a samu ba, to babu wanda za a rantsar a ranar 29 ga watan Mayu.

Ita kuwa jam’iyyar LP ta bayyana cewa ya kamata a soke zaben shugaban kasa na 2023.

Jam’iyyar ta yi kira da a soke zaben shugaban kasar ne bisa ce-ce-kucen da ake yi dangane da kashi 25 na kuri’un da aka kada a jihohin Nijeriya ciki har da Abuja, babban birnin tarayya.

Babban mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben Obi-Datti, Yunusa Tanko, ya bayyana haka a lokacin da yake mayar da martani kan karar da ke neman a dakatar da rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban kasar Nijeriya.

Tanko ya bayyana cewa jam’iyyar da dan takararta na shugaban kasa, Peter Obi, na sa ran ganin yanayin da kotu ta amince a rantsar da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, har sai an zabi shugaban kasa nagari.

Ya ce, “Abin da na sani shi ne, za a rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu idan har muka kasa samun nasara a kotun sauraron kararrakin zabe, rantsuwar za ta shafi shugaban kasa ne kawai. Wannan yana cikin sashe na 146 (2) na kundin tsarin mulki.

“Addu’armu ita ce a soke zaben, a kuma bayyana cewa babu shi. Wannan matsayi ya kasance ne tun da dan takarar APC bai samu kashi 25 a jihohin Nijeriya ciki har da Abuja. Idan an fayyace shi sosai, ya ba da ikon sashe na 146 na kundin tsarin mulkin kasa wanda ya ce “Idan babu shugaban kasa, shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ne zai karbi ragamar mulki”. Idan har shari’ar nan ta tafi yadda muke addu’a, abin da ake nufi shi ne Lawan zai karbi ragamar shugabancin tarayyar Nijeriya.

“Idan kuma Lawan bai dawo a matsayin shugaban majalisar dattawa ba ta 10 ba, dole ne ya mika wa zababben shugaban majalisar dattawa da za a kaddamar a watan Yuni, sannan zai bukaci a ba shi watanni tara domin gudanar da sabon zaben shugaban kasar. Haka ya kamata domin guje wa rudani a ko’ina.”

Sai dai kuma, rundunonin tsaron Nijeriya musamman na soja da ‘yansanda sun yi gargadi ga masu neman kawo rudani game da mika ragamar mulki a karshen watannan, suna masu cewa za su dauki matakin ba-sani-ba-sabo a kan ko ma waye da ke neman yin kafar ungulu ga shirin na mika mulki.

Rundunar sojojin Nijeriya da babban sufetan ‘yansandan Nijeriya, Usman Baba sun gargadi ‘yan siyasar da ke kokarin kawo rudani a kasa gami da kokarin kawo cikas ga bikin rantsar da sabon zababben shugaban kasa, Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Babban daraktan yada labarai na shalkwatar tsaro ta kasa, Bigediya Janar Tukur Gusau ya gargadi kungiyoyin da ke barazanar hargiza bikin rantsarwar da yunkurin lalata tsarin dimokuradiyyar da Nijeriya ke kai da su janye domin hukumomi ba za su lamunci hakan ba.

Haka nan shi ma Babban Hafsan Sojojin Kasa, Laftanar Janar Faruk Yahaya ya yi barazanar kawar da duk wani yunkuri da zai shafi matsalar tsaron kasa, ya kuma gargadi masu yunkurin kawo cikas da ka da su fara, don kuwa sojoji za su gama da su.

A nata bangaren, rundunar ‘yansandan Nijeriya ta ce tana nan tana sanya idanu kan ’yan siyasar da ke kokarin kawo tsaiko ko kuma cikas game da rantsar da sabuwar gwamnatin a ranar 29 ga watan Mayu.

A wani taron manema labarai a shalkwatarsu, Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya, Usman Baba ne ya bayyana cewa sun lura da wasu ‘yan siyasar da sakamakon zaben 2023 bai yi musu dadi ba na yin kalamai na tunzura jama’a, wanda hakan ka iya zama barazana ga bikin rantsar da shugaban kasa a ranar 29 ga Mayu da muke ciki.

“Rundunar ‘yansandan Nijeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron leken asiri na kasa, suna sanya idanu sosai kan ayyukan wadannan jiga-jigan ‘yan siyasan da ma sauran wadansu marasa kishin kasa, wadanda a ko da yaushe suke burin ganin kasar ta fada cikin hali na tashin hankali da rashin zaman lafiya.

“Jami’an tsaro ba za su lamunci irin wadannan furuci da ka iya jefa kasar nan cikin rudani ba, duk wani dan siyasa da ya yi kunnen uwar shegu da gargadin, zai fuskanci fushin hukuma.” In ji shi.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Yadda Za A Dakile Kitsa Labarun Kanzon Kurege A Nijeriya  -Keyamo

Yadda Za A Dakile Kitsa Labarun Kanzon Kurege A Nijeriya  -Keyamo

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.