Akalla kauyuka 15 ne suka zama kufai a ƙaramar hukumar Dandume ta Jihar Katsina, sakamakon ƙara tsananta hare-haren ’yan bindiga a yankin.Mazauna yankin sun shaida wa BBC cewa hare-haren sun ƙaru a ƙananan hukumomin Funtua, Dandume da Bakori, musamman a al’ummomin kudancin jihar.
Sun ce tabarbarewar tsaro ta jefa su cikin fargaba, tare da takaita zirga-zirga da kuma kawo cikas ga harkokin noma da sauran ayyukan tattalin arziki.
Wani mazaunin Funtua ya shaida wa BBC cewa ’yan bindiga na kai hare-hare a wasu sassan garin duk da kasancewar jami’an tsaro a yankin.
Ya ce, “Sai dai jami’an tsaron suna ƙoƙari. Duk lokacin da aka kira su, suna amsawa kuma su taimaka.”
A ƙaramar hukumar Bakori kuwa, mazauna sama da garuruwa da kauyuka 10, ciki har da Kakumi, Sabon Layi, Gidan Jaura da Garanguzai, sun nuna damuwa kan ci gaba da kai hare-haren.
Wani mazaunin yankin ya ce ’yan bindigar sun sanya zirga-zirga tsakanin al’ummomin yankin cikin haɗari.
A Ɗandume kuma, wani mazaunin yankin ya ce lamarin tsaron ya ƙara dagulewa, inda ya zargi ’yan bindiga da kai hare-hare kusan kullum.
Ya yi zargin cewa sama da mutane 100 aka yi garkuwa da su a yankin cikin makonni biyu kacal, yayin da da dama daga cikinsu suke hannun masu garkuwa da mutanen har yanzu.
Wani mazaunin Dandume ya tabbatar da cewa kusan kauyuka 15 ne suka zama Kango saboda tsananin barazanar hare-haren ’yan bindiga.














