• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Gami Da Kashe Wani Lauya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a tantance ko su wane ne ba sun yi garkuwa da wani lauya Nnewi da ke Jihar Anambra, Jude Oguejiofor tare da kashe shi.

An ce ‘yan bindigar sun kai farmaki gidansa ne da misalin karfe 1 na safe a unguwar Orsumogu da ke Karamar Hukumar Ihiala, yayin da suke harbe-harbe a iska domin su tafi da shi da kanensa, wani likita.

  • Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi
  • Jakadan Sin Ya Jaddada Aniyar Kasarsa Game Da Ba Da Gudummawar Shawo Kan Rikicin Siyasar Yemen

PUNCH Metro ta samu labarin cewa Oguejiofor wanda ya fito daga Osumoghu a Karamar Hukumar Ihiala ta Anambra, yana zaune ne a Nnewi da ke Karamar Hukumar Nnewi ta Arewa a jihar.

Ya tsaya takarar dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Ihiala a zaben 2023 karkashin jam’iyyar Peoples Democratic Party. per Eagles Lose Wata majiya mai tushe da ta nemi a sakaya sunanta, wacce ta tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, Majiyar ta ce yayin da aka saki kanin washegari, ‘yan ta’addan sun tsare lauyan inda suka bayar da hujjar cewa suna bincikensa ne saboda sun samu labarin ya fallasa bayanan ayyukansu ga gwamnatin jihar.

Ya ce, “Na kan bi Jude gida ne domin in ziyarci iyayensa, kuma bai taba samun wata matsala da ‘yan bindigar a unguwarsu ba. Hakika, duk lokacin da na raka shi gida, sai su bincika ni, amma ba sa binciken Yahuda.

“Lokacin da ya koma gida tare da dan uwansa wanda ya sayi sabuwar mota kirar Ledus Jeep, ba shi da wata matsala da kowa sai kawai muka ji an sace su biyun.

“Daga baya ‘yan bindigar sun sako dan uwansa kuma suka ci gaba da tuhumarsa da cewa yana rubuta koke ga Gwamnatin Jihar Anambra kan ayyukansu. Sai dai sun yi alkawarin za a sake shi da zarar sun kammala bincike.

Ya ce daga baya sun tuntubi ‘yan uwa bayan ‘yan kwanaki inda suka ce su manta da batun sakin lauyan domin kuwa sun kashe shi.

“A ranar ne muka ji labarin cewa mahaifinsa ya fadi ya mutu nan take da jin labarin faruwar lamarin bayan da ‘yan bindigar suka tuntubi ‘yan uwa suka sanar da su cewa sun kashe lauyan.”

Sai dai da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Anambra, DSP Tochukwu Ikenga, bai tabbatar da faruwar lamarin ba, domin ya ce yana cikin wani taro.

Garin Ihiala dake kan iyaka tsakanin jihohin Anambra da Imo na daga cikin yankunan da matsalar tsaro ta fi kamari a yankin Kudu maso Gabas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Kama Magidanci Da Tan 7.6 Na Miyagun Kwayoyi

Next Post

Hakuri Shi Ne Babban Sirrin Samun Nasarar Kowacce Sana’a –Khadija Bello

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

7 days ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
Next Post
Hakuri Shi Ne Babban Sirrin Samun Nasarar Kowacce Sana’a –Khadija Bello

Hakuri Shi Ne Babban Sirrin Samun Nasarar Kowacce Sana’a –Khadija Bello

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.