ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC

by Yusuf Shuaibu
1 month ago

Zangon farko na zaɓen 2027, ya nuna cewa ƴan majalisar wakilai guda 50 na majalisa ta 10 ba za su kasance a zauren majalisa ta 11 ba.

A lokacin buga wannan rahoton, aƙalla ƴan majalisar wakilai 48 na jam’iyyar APC sun sha kaye a zaɓen fid da gwani da aka gudanar a faɗin ƙasar a ƙarshen mako. Yayin da ƴan majalisa biyu na Bayelsa ba su shiga takara ba, saboda suna neman manyan muƙaman siyasa.

Ana sa ran adadin zai ƙaru, saboda har yanzu APC ba ta fitar da cikakken sakamakon zaɓukan fid da gwani ba, kuma sauran jam’iyyun adawa kamar jam’iyyar NDC da PDP da LP da ADC da APGA da sauransu ba su gudanar da zaɓukan fitar da gwani ba.

ADVERTISEMENT

Sai dai kuma, shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas da mataimakinsa, Benjamin Kalu sun jagoranci ƴan majalisar dokoki na APC da suka samu tikitin dawowa.

Manyan ƴan majalisar APC da suka rasa tikiti a zaɓen fitar da gwani sun haɗa da Nicholas Mutu (Bomadi/Patani, Jihar Delta, wanda ya kasance a majalisa tun 1999) da Mike Etaba (Obubra/Etung, Jihar Kuros Ribas), wanda ya rasa tikitin komawa majalisa karo na huɗu.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Haka kuma shi ma, Farfesa Julius Ihonɓbere, shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, yana cikin ƴan majalisar da ba za su dawo ba. Shi ma ɗan majaisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Pankshin/Kanke/Kanam, Yusuf Adamu Gagdi, ya rasa tikiti na neman wa’adi na uku.

A Jihar Borno kuwa, Usman Zannah (Gubio/Kaga/Magumeri) da Betara Aliyu (Biu/Shani/Kwaya Kusar/Bayo) da Kadiri Rahis (wakilin Maiduguri da kewaye) da Satomi Ahmed (Jere) da Bukar Talba (Marte/Monguno/Nganzai) da Ahmed Jaha (Gwoza/Chibok/Damboa), duk sun gaza masan tikiti.

A Jihar Bayelsa, mambobi biyu da suka riƙe muƙamansu sun ci gaba da samun tikitin jam’iyya a mazaɓar tarayya ta Yenagoa/Kolokuma-Opukuma da ɗan majalisar Oforji Oboku, ya samu tikitin jam’iyyar. Haka ma a mazaɓar Ijaw ta kudu, Injiniya Rodney Ambaiowei, wanda shi ne ɗan majalisa mai ci, shi ma ya yi nasara.

A mazaɓar Ogbia, Jude Reɗ Ogbuku ya lashe tikitin ɗan majalisar wakilai, yayin da Matema Obodor na PDP, wanda ke riƙe da muƙamin ɗan majalisar, ya ki canja sheƙa tare da Gwamna Douye Diri zuwa APC.

A mazaɓar Nembe/Brass, Jonathan Robinson Obuebite ya sami tikitin APC. Ita ma ƴar majalisa, Marie Ebikake, ita ma ta zaɓi ta ci gaba da zama a PDP domin tsayawa takarar majalisar dattawa a mazaɓar Bayelsa ta yamma.

Yayin da a Jihar Kuros Ribas, ƴan majalisar wakilai guda biyar daga cikin takwas sun sha kashi.

Daga cikin waɗanda suka gaza samun tikiti akwai ƴan majalisa masu wa’adi da dama a majalisar tarayya da suka haɗa da mamba mai wa’adi uku, Mike Etaba, wanda ke wakiltar Obubra/Etung da mamba mai wa’adi biyu, Aleɗ Egbona, wanda ke wakiltar Abi/Yakurr, wanda ya sauya sheƙa zuwa PDP kafin wa’adin ƙarshe da mamba mai wa’adi ɗaya, Godwin Offiono, wanda ke wakiltar mazaɓar Ogoja/Yala da mamba mai wa’adi ɗaya, Emil Inyang, wanda ke wakiltar mazaɓar Akamkpa/Biase da mamba mai wa’adi ɗaya, Bassey Akiba, wanda ke wakiltar Odukpani/ Calabar.

A Akwa Ibom, ko da yake APC ba ta fitar da sakamako a hukumance ba, rahotanni sun nuna cewa shi kaɗai Okpolupum Etteh, wanda yake wakiltar mazaɓar Eket/Esit Eket/Ibeno, ya sha kashi.

A Jihar Ribas, waɗanda suka yi rashin nasara sun haɗa da John Azubuike Opara da Anderson Allison Igbiki, Awaji Imombek Abiante, da Boma Goodhead (a halin yanzu suna wakiltar mazaɓun Andoni/Opobo da Asari-Toru a majalisar wakilai).

A Jihar Delta, waɗanda suka sha kaye a yanzu su ne Nicholas Mutu, Bomadi/Patani da Ngozi Lawrence Okolie, wacce ta sha kaye a zaɓen mazaɓar tarayya ta Aniocha/Oshimili.

A Jihar Ekiti, ƴan majalisa uku da ke kan karagar mulki sun faɗi yayin zaɓen fid da gwanin na jam’iyya APC.

A mazaɓar Ekiti ta tsakiya, Oladapo Karounwi, ya samu ƙuri’u 6,573, wanda yake kan kujerar, Abiodun Omoleye, ya samu ƙuri’u 2,096. A mazaɓar Ekiti ta kudu, Okoro Toyin Zaccheaus ya samu ƙuri’u 9,798, wanda ya doke mai riƙe da muƙamin, Rufus Adeni Ojuawo, wanda ya samu ƙuri’u 1,842. A mazaɓar Ekiti ta arewa II, Ibrahim Olanrewaju ya samu ƙuri’u 6,856 wanda ya doke mai riƙe da muƙamin, wanda ya samu ƙuri’u 2,102.

A Jihar Ogun, biyar daga cikin ƴan majalisa tara da ke kan muƙamansu sun kasa samun tikitin komawa majalisar wakilai. Daga cikin waɗanda suka sha kaye a akwai Ishaƙ Akinlade na mazaɓar Yewa ta arewa /Ipokia da Ibrahim Isiaka, wanda ke wakiltar mazaɓar Ifo/Ewekoro da Tunji Akinosi mai wakiltar mazaɓar Ado-Odo/Ota da Femi Ogunbanwo da ke wakiltar mazaɓar Ijebu Ode/Ijebu North East/Odogbolu.

A Jihar Ondo, akwai tashin hankali a cikin APC bayan kwamitin zaɓen fitar da gwani mai mambobi bakwai ya kasa bayyana sakamakon zaɓen fid da gwani na majalisar wakilai na ranar Asabar da ta gabata.

A Jihar Legas, wani ɗɗan takarar da ke neman kujerar majalisar wakilai a mazaɓar Epe, Mista Ademola Amure, ya yi kira da a soke zaɓen fid da gwani na APC da aka yi ranar Asabar a mazaɓar, yana kwatanta zaɓen a matsayin mara tsari da ke cike da manyan kura-kurai da kuma maguɗi.

Haka nan, a mazaɓar Iwo, Mista Ademola Habeeb ya samu tikiti ta hayar masalaha, yayin da Mista Asalu Daɓid ya samu tikiti ta hayar masalaha a jam’iyyar APC a mazaɓar Ede.

Dakta Obawale Adebisi ya samu tikiti ta hayar masalaha a mazaɓar Ila, yayin da ɗan majalisa mai ci Mista Taofeek Ajilesoro na mazaɓar Ife shi ma ya samu titiki ta hanyar masalaha.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
Next Post
Taron Ministocin Cinikayya Na APEC Ya Yi Kira Da A Samar Da Matsaya Daya Ta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya

Taron Ministocin Cinikayya Na APEC Ya Yi Kira Da A Samar Da Matsaya Daya Ta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.