ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yana Da Kyau Matasa Su Rika Shiga Harkar Kudaden Crypto – Farfesa

by Sadiq
4 years ago
Matasa

Farfesa Aliyu Abdullahi Jibiya, daga Jami’ar Bayero ta Kano, ya yi kira ga matasa da su ci gajiyar kasuwanci da kudaden Intanet da suka mamaye duniya a wannan lokacin.

Farfesa Jibiya ya bayyana cewar kudin kasuwanci na Intanet mai suna ZUGACOIN daya ne daga cikin wadan da suka fi shahara a harkar kudin Intanet a duniya.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor
  • Da Dumi-Dumin: Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ekiti Ya Rasu Yana Da Shekaru 66

Aliyu Jibiya, ya bayyana haka ne a yayin tattaunwa da Jaridar Daily Post, a yayin bikin karrama shugaban gidauniyar SAMZUGA, wanda ya shahara wajen hadahadar kasuwanci da kudaden Intanet.

ADVERTISEMENT

Jibiya ya bayyana cewa, “Archbishop Farfesa SamZuga wanda yake jami’in diflomasiyya a tsarin ‘INTERNATIONAL SOCIETY OF DIPLOMATS AND GLOBAL EMISSARY COUNCIL’, wanda shi ne shugaban kula da sasheb tattalin arziki na farko a tsarin IT na duniya.”

“Samzuga na cikin farko-farko a fannin tattalin arziki a tsarin kudin Intanet na duniya, kuma shi ne farkon wanda ya kafa cibiyar hada-hadar kasuwanci a Afirka.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Gombe Ya Buƙaci Kamfanin Simintin Ashaka Ya Gyara Hanyoyin Da Manyan Motoci Suka Lalata

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Farfesa Jibiya, ya kuma kara da cewa, “Samzuga wanda ya samar da kudin ZUGACOIN, na daya daga cikin kamfanoni uku da suka fi shahara a harkar kudin Intanet a tsakanin ‘yan Nijeriya da ke a wasu kasashen duniya.”

“Archibishop Farfesa Sam Zuga, limamin coci ne a Nijeriya da ke zaune a Dubai, dan kasuwa ne mai taimakon jama’a, ya samu lambar yabo ta digirin girmamawa daga jami’o’i daban-daban a duniya, ciki har da wasu jami’o’in kasar Amurka.”

“Haka kuma, Archbishop Farfesa SamZuga, mamba ne a kungiyar ‘yan kasuwa ta Dubai, kuma dan Nijeriya na biyu da ya karbi lambar yabo daban-daban a fannin zaman lafiya a kokarinsa na samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al’umma a ciki da wajen Nijeriya, haka kuma, an taba ba shi lambar yabo ta Jakadan Majalisar Dinkin Duniya kan zaman lafiya.

“Archbishop Farfesa SamZuga, yana da lasisi a Dubai wanda ke ba shi damar shigo da zinari daga sassan duniya zuwa Dubai, kuma shi ne ya samar cibiyar kasuwanci ta Intanet don kawo shirye-shiryen sauyin yanayi wanda aka sanar a hukumance a taron sauyin yanayi na Majalisar Dinkin Duniya, wannan manufar ita ce kawar da radadin matsin lamba na rayuwa ga masu karamin karfi.”

A jawabinsa yayin karbar lambar yabo, Farfesa Mkpa Ogoh Mkpa, wanda ya wakilci Archbishop Farfesa Sam Zuga, ya gode wa Ubangiji Madaukakin Sarki da gaisuwa ta musamman bisa karramawar da aka yi masa, ya kuma tabbatar da cewa Archbishop Farfesa Sam zai ci gaba da yin iya kokarinsa, zai kara himma wajen samar da sabbin abubuwa don ciyar da al’umma gaba kamar yadda ya saba.

MASU ALAKA

Gwamnan Gombe Ya Buƙaci Kamfanin Simintin Ashaka Ya Gyara Hanyoyin Da Manyan Motoci Suka Lalata
Kananan Labarai

Gwamnan Gombe Ya Buƙaci Kamfanin Simintin Ashaka Ya Gyara Hanyoyin Da Manyan Motoci Suka Lalata

August 18, 2026
MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Next Post
Hauhawar Farashi Ya Karu Da Kashi 20.77 A Nijeriya

Hauhawar Farashi Ya Karu Da Kashi 20.77 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.