• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yana Da Kyau Matasa Su Rika Shiga Harkar Kudaden Crypto – Farfesa

by Sadiq
5 months ago
in Kananan Labarai
0
Yana Da Kyau Matasa Su Rika Shiga Harkar Kudaden Crypto – Farfesa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Farfesa Aliyu Abdullahi Jibiya, daga Jami’ar Bayero ta Kano, ya yi kira ga matasa da su ci gajiyar kasuwanci da kudaden Intanet da suka mamaye duniya a wannan lokacin.

Farfesa Jibiya ya bayyana cewar kudin kasuwanci na Intanet mai suna ZUGACOIN daya ne daga cikin wadan da suka fi shahara a harkar kudin Intanet a duniya.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor
  • Da Dumi-Dumin: Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ekiti Ya Rasu Yana Da Shekaru 66

Aliyu Jibiya, ya bayyana haka ne a yayin tattaunwa da Jaridar Daily Post, a yayin bikin karrama shugaban gidauniyar SAMZUGA, wanda ya shahara wajen hadahadar kasuwanci da kudaden Intanet.

Jibiya ya bayyana cewa, “Archbishop Farfesa SamZuga wanda yake jami’in diflomasiyya a tsarin ‘INTERNATIONAL SOCIETY OF DIPLOMATS AND GLOBAL EMISSARY COUNCIL’, wanda shi ne shugaban kula da sasheb tattalin arziki na farko a tsarin IT na duniya.”

“Samzuga na cikin farko-farko a fannin tattalin arziki a tsarin kudin Intanet na duniya, kuma shi ne farkon wanda ya kafa cibiyar hada-hadar kasuwanci a Afirka.”

Labarai Masu Nasaba

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna

NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai

Farfesa Jibiya, ya kuma kara da cewa, “Samzuga wanda ya samar da kudin ZUGACOIN, na daya daga cikin kamfanoni uku da suka fi shahara a harkar kudin Intanet a tsakanin ‘yan Nijeriya da ke a wasu kasashen duniya.”

“Archibishop Farfesa Sam Zuga, limamin coci ne a Nijeriya da ke zaune a Dubai, dan kasuwa ne mai taimakon jama’a, ya samu lambar yabo ta digirin girmamawa daga jami’o’i daban-daban a duniya, ciki har da wasu jami’o’in kasar Amurka.”

“Haka kuma, Archbishop Farfesa SamZuga, mamba ne a kungiyar ‘yan kasuwa ta Dubai, kuma dan Nijeriya na biyu da ya karbi lambar yabo daban-daban a fannin zaman lafiya a kokarinsa na samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al’umma a ciki da wajen Nijeriya, haka kuma, an taba ba shi lambar yabo ta Jakadan Majalisar Dinkin Duniya kan zaman lafiya.

“Archbishop Farfesa SamZuga, yana da lasisi a Dubai wanda ke ba shi damar shigo da zinari daga sassan duniya zuwa Dubai, kuma shi ne ya samar cibiyar kasuwanci ta Intanet don kawo shirye-shiryen sauyin yanayi wanda aka sanar a hukumance a taron sauyin yanayi na Majalisar Dinkin Duniya, wannan manufar ita ce kawar da radadin matsin lamba na rayuwa ga masu karamin karfi.”

A jawabinsa yayin karbar lambar yabo, Farfesa Mkpa Ogoh Mkpa, wanda ya wakilci Archbishop Farfesa Sam Zuga, ya gode wa Ubangiji Madaukakin Sarki da gaisuwa ta musamman bisa karramawar da aka yi masa, ya kuma tabbatar da cewa Archbishop Farfesa Sam zai ci gaba da yin iya kokarinsa, zai kara himma wajen samar da sabbin abubuwa don ciyar da al’umma gaba kamar yadda ya saba.

Tags: CryptoFarfesaKudaden IntanetZugaCoin
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutum Dubu 100 Tare Da Tarwatsa Mutane Miliyan 2 —Irabor

Next Post

Hauhawar Farashi Ya Karu Da Kashi 20.77 A Nijeriya

Related

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna
Kananan Labarai

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna

3 days ago
NIS
Kananan Labarai

NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai

5 days ago
INEC Ta Kara Wa’adin Karbar Katin Zabe
Kananan Labarai

Zaben Gwamnoni: Ku Ankare Akwai Masu Shaidar Aikin Tsaro Ta Bogi, INEC Ga Masu Zabe

1 week ago
Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4
Kananan Labarai

Shugabar Matan NNPP Reshen Abuja Ta ‘Yanta Fursunoni 4

1 month ago
Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil
Kananan Labarai

Dan’asabe Ya Janye Kalaman Da Ya Yi A Kan Babban Asibitin Wudil

2 months ago
Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara
Kananan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

2 months ago
Next Post
Hauhawar Farashi Ya Karu Da Kashi 20.77 A Nijeriya

Hauhawar Farashi Ya Karu Da Kashi 20.77 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

March 27, 2023
Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.