Ƙungiyar kare haƙƙin Musulmi ta Muslim Rights Concern (MURIC) ta zargi Gwamnatin Tarayya da nuna wariya ta fuskar addini, inda ta ce ana fifita Kiristoci fiye da Musulmi a wasu manufofi da ayyuka.
A cikin wata sanarwa da daraktan ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar, MURIC ta bayyana cewa wasu matakai da gwamnati ke ɗauka na nuna son kai, musamman batun gina wata cibiyar ibada ta Kiristoci mai tsadar kusan naira biliyan 25 a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja. 
Ƙungiyar ta kuma soki yadda aka raba tallafin kuɗi ga waɗanda rikice-rikice suka shafa a wasu jihohi, tana mai cewa an ba wasu yankuna fifiko ba tare da bai wa wasu masu irin wannan matsala kulawa iri ɗaya ba. 
MURIC ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta yi bayani kan waɗannan matakai, tana mai jaddada cewa Musulman Nijeriya na da haƙƙin samun adalci da daidaito a dukkan al’amuran gwamnati. 
Sai dai irin waɗannan zarge-zarge na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan batun daidaito tsakanin addinai a Nijeriya, ƙasa mai cike da mabambantan addinai da al’adu.















Discussion about this post