ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

by Muhammad
1 month ago

Majalisar Dattawa ta buƙaci a ɗauki matakan gaggawa domin cike gibin da ke cikin tsarin yaki da annobar cututtuka a Nijeriya, bayan tabbatar da sabbin kamu wa da cutar COVID-19 a Jihar Cross River.

Kudirin ya fito ne daga Sanata Ipalibo Banigo, inda ta tunatar da cewa Sashe na 14(2)(b) na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima) ya ɗora wa gwamnati alhakin tabbatar da tsaro da jin walwalar jama’a, ciki har da kare lafiyar al’umma.

Ta bayyana damuwa cewa tsawon lokacin da aka ɗauka kafin bayyanar cutar ya wuce abin da aka saba gani, lamarin da ke sanya fargabar yaduwar cutar a cikin al’umma. Ta kuma ce an gano wasu da ake zargi da kamuwa, kuma ana ci gaba da bibiyar waɗanda suka yi hulɗa da su.

ADVERTISEMENT

Sanatar ta jaddada cewa daukar matakai kan irin waɗannan annoba na buƙatar wadatattun kayan aiki kamar na’urorin gwaji da sinadarai, da kayan kariya ga ma’aikatan lafiya.

Sai dai ta yi gargadin cewa Hukumar Kula da Cututtuka ta Ƙasa, NCDC, na fuskantar ƙalubale saboda jinkirin sakin kuɗaɗe da matsalolin saye da ƙarancin kasafin kuɗi tun daga 2025.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

Ta tunatar kan darussan da aka koya daga annobar COVID-19, zazzabin Lassa da shirye-shiryen tunkarar Ebola, inda ta ce jinkirin gano cuta da rashin haɗin kai na iya ƙara cutar da lafiyar jama’a da tsaron ƙasa.

Bayan tattaunawa, Majalisar ta buƙaci Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya da NCDC su ƙara ƙaimi wajen sa ido, gwaje-gwaje da bibiyar masu hulɗa da marasa lafiya bisa ƙa’idojin ƙasa.

Haka kuma ta roƙi Ma’aikatar Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki da ta gaggauta sakin kuɗaɗe tare da la’akari da buɗe hanyoyin tallafin gaggawa domin tunkarar annobar.

Majalisar ta kuma nemi cikakken rahoto daga NCDC kan matsayin shirin ƙasar, ciki har da yawan kayan aiki, dakunan gwaje-gwaje da shirye-shiryen tunkarar annoba.

Ta ƙara da kira ga a ƙarfafa wayar da kan jama’a a faɗin ƙasa domin hana yaɗuwar jita-jita da rage tsoro, tare da ƙarfafa bin matakan kariya.

Haka kuma ta buƙaci gwamnatocin jihohi su ƙarfafa shirye-shiryensu ta hanyar inganta tsarin sa ido, gaggawar daukar martani da saka hannun jari a harkar lafiya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya yaba wa masu gabatar da kudirin, yana mai cewa za a miƙa shawarwarin majalisar ga hukumomin da abin ya shafa domin ɗaukar matakin gaggawa.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Baje Kolin Canton Fair Karo Na 139 Ya Hallara Masu Sayayya Na Ketare Kimanin 245,000

Baje Kolin Canton Fair Karo Na 139 Ya Hallara Masu Sayayya Na Ketare Kimanin 245,000

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.