Majalisar Dattawa ta buƙaci a ɗauki matakan gaggawa domin cike gibin da ke cikin tsarin yaki da annobar cututtuka a Nijeriya, bayan tabbatar da sabbin kamu wa da cutar COVID-19 a Jihar Cross River.
Kudirin ya fito ne daga Sanata Ipalibo Banigo, inda ta tunatar da cewa Sashe na 14(2)(b) na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima) ya ɗora wa gwamnati alhakin tabbatar da tsaro da jin walwalar jama’a, ciki har da kare lafiyar al’umma.
Ta bayyana damuwa cewa tsawon lokacin da aka ɗauka kafin bayyanar cutar ya wuce abin da aka saba gani, lamarin da ke sanya fargabar yaduwar cutar a cikin al’umma. Ta kuma ce an gano wasu da ake zargi da kamuwa, kuma ana ci gaba da bibiyar waɗanda suka yi hulɗa da su.
Sanatar ta jaddada cewa daukar matakai kan irin waɗannan annoba na buƙatar wadatattun kayan aiki kamar na’urorin gwaji da sinadarai, da kayan kariya ga ma’aikatan lafiya.
Sai dai ta yi gargadin cewa Hukumar Kula da Cututtuka ta Ƙasa, NCDC, na fuskantar ƙalubale saboda jinkirin sakin kuɗaɗe da matsalolin saye da ƙarancin kasafin kuɗi tun daga 2025.
Ta tunatar kan darussan da aka koya daga annobar COVID-19, zazzabin Lassa da shirye-shiryen tunkarar Ebola, inda ta ce jinkirin gano cuta da rashin haɗin kai na iya ƙara cutar da lafiyar jama’a da tsaron ƙasa.
Bayan tattaunawa, Majalisar ta buƙaci Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya da NCDC su ƙara ƙaimi wajen sa ido, gwaje-gwaje da bibiyar masu hulɗa da marasa lafiya bisa ƙa’idojin ƙasa.
Haka kuma ta roƙi Ma’aikatar Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki da ta gaggauta sakin kuɗaɗe tare da la’akari da buɗe hanyoyin tallafin gaggawa domin tunkarar annobar.
Majalisar ta kuma nemi cikakken rahoto daga NCDC kan matsayin shirin ƙasar, ciki har da yawan kayan aiki, dakunan gwaje-gwaje da shirye-shiryen tunkarar annoba.
Ta ƙara da kira ga a ƙarfafa wayar da kan jama’a a faɗin ƙasa domin hana yaɗuwar jita-jita da rage tsoro, tare da ƙarfafa bin matakan kariya.
Haka kuma ta buƙaci gwamnatocin jihohi su ƙarfafa shirye-shiryensu ta hanyar inganta tsarin sa ido, gaggawar daukar martani da saka hannun jari a harkar lafiya.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya yaba wa masu gabatar da kudirin, yana mai cewa za a miƙa shawarwarin majalisar ga hukumomin da abin ya shafa domin ɗaukar matakin gaggawa.















Discussion about this post