Mafi yawancin alhazan Nijeriya da ke shirin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026, sun tsinci kansu cikin tsaka-mai-wuya wajen samun damar shiga Rawdah da ke cikin Masallacin Manzon Allah (S.A.W) a birnin Madina.
Wannan matsala ta samo asali ne sakamakon tsarin yin rajista ta hanyar manhajar “Nusuk” wadda hukumomin Saudiyya suka samar domin tsara ziyara.
An ruwaito cewa an hana wasu alhazai, musamman daga jihohin Oyo da Jigawa, shiga wannan waje mai alfarma saboda rashin yin rajista a manhajar kafin isa wajen.
Wannan yanayi ya fi shafar tsofaffi, la’akari da tsananin zafi da kuma wahalar zirga-zirga a cikin masallacin.
Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana cewa sun kwashe kwanaki da dama a Madina ba tare da sun samu damar shiga Rawdah ba, lamarin da ya jefa su cikin fargabar barin birnin zuwa Makkah ba tare da sun ziyarci wajen ba.
Haka kuma, sun koka kan cewa manhajar tana da sarƙaƙiya da kuma wahalar amfani.
To sai dai, wasu jami’ai sun bayyana cewa tsarin yana tafiya yadda ya kamata matuƙar an bi ƙa’idojin da aka shimfiɗa.
Muhammad Aliyu, ɗaya daga cikin jami’an Amirul Hajj, ya tabbatar da cewa ya samu nasarar yin rajista ta manhajar, har ma ya taimaka wa wasu maniyyatan wajen ganin sun samu damar shiga.
A gefe guda kuma, wasu maniyyatan sun samu nasarar shiga Rawdah ta wasu ƙofofi daban bayan sun shafe lokaci suna jira, duk da cewa hakan ba ya cikin tsarin da hukuma ta amince da shi.
Rahotanni sun nuna cewa ƙarancin faɗakarwa da rashin horar da maniyyata kan yadda ake amfani da sabbin fasahohi na ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka haddasa wannan tsaiko.
A halin yanzu, fargaba ta mamaye zukatan maniyyata da dama kan yiwuwar barin Madina ba tare da sun gudanar da ziyara a Rawdah ba, wadda ake ɗauka ɗaya daga cikin mafi muhimmancin wurare a Musulunci.















Discussion about this post