ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2026: Alhazan Nijeriya Na Fuskantar Ƙalubalen Shiga Rawdah A Madina Saboda Matsalar Manhaja

by Sadiq
4 weeks ago

Mafi yawancin alhazan Nijeriya da ke shirin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026, sun tsinci kansu cikin tsaka-mai-wuya wajen samun damar shiga Rawdah da ke cikin Masallacin Manzon Allah (S.A.W) a birnin Madina.

Wannan matsala ta samo asali ne sakamakon tsarin yin rajista ta hanyar manhajar “Nusuk” wadda hukumomin Saudiyya suka samar domin tsara ziyara.

ADVERTISEMENT

An ruwaito cewa an hana wasu alhazai, musamman daga jihohin Oyo da Jigawa, shiga wannan waje mai alfarma saboda rashin yin rajista a manhajar kafin isa wajen.

Wannan yanayi ya fi shafar tsofaffi, la’akari da tsananin zafi da kuma wahalar zirga-zirga a cikin masallacin.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana cewa sun kwashe kwanaki da dama a Madina ba tare da sun samu damar shiga Rawdah ba, lamarin da ya jefa su cikin fargabar barin birnin zuwa Makkah ba tare da sun ziyarci wajen ba.

Haka kuma, sun koka kan cewa manhajar tana da sarƙaƙiya da kuma wahalar amfani.

To sai dai, wasu jami’ai sun bayyana cewa tsarin yana tafiya yadda ya kamata matuƙar an bi ƙa’idojin da aka shimfiɗa.

Muhammad Aliyu, ɗaya daga cikin jami’an Amirul Hajj, ya tabbatar da cewa ya samu nasarar yin rajista ta manhajar, har ma ya taimaka wa wasu maniyyatan wajen ganin sun samu damar shiga.

A gefe guda kuma, wasu maniyyatan sun samu nasarar shiga Rawdah ta wasu ƙofofi daban bayan sun shafe lokaci suna jira, duk da cewa hakan ba ya cikin tsarin da hukuma ta amince da shi.

Rahotanni sun nuna cewa ƙarancin faɗakarwa da rashin horar da maniyyata kan yadda ake amfani da sabbin fasahohi na ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka haddasa wannan tsaiko.

A halin yanzu, fargaba ta mamaye zukatan maniyyata da dama kan yiwuwar barin Madina ba tare da sun gudanar da ziyara a Rawdah ba, wadda ake ɗauka ɗaya daga cikin mafi muhimmancin wurare a Musulunci.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Manufar Cire Haraji Za Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

Manufar Cire Haraji Za Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.