ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2026: Alhazan Nijeriya Na Fuskantar Ƙalubalen Shiga Rawdah A Madina Saboda Matsalar Manhaja

by Sadiq
2 months ago

Mafi yawancin alhazan Nijeriya da ke shirin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026, sun tsinci kansu cikin tsaka-mai-wuya wajen samun damar shiga Rawdah da ke cikin Masallacin Manzon Allah (S.A.W) a birnin Madina.

Wannan matsala ta samo asali ne sakamakon tsarin yin rajista ta hanyar manhajar “Nusuk” wadda hukumomin Saudiyya suka samar domin tsara ziyara.

ADVERTISEMENT

An ruwaito cewa an hana wasu alhazai, musamman daga jihohin Oyo da Jigawa, shiga wannan waje mai alfarma saboda rashin yin rajista a manhajar kafin isa wajen.

Wannan yanayi ya fi shafar tsofaffi, la’akari da tsananin zafi da kuma wahalar zirga-zirga a cikin masallacin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Wasu daga cikin maniyyatan sun bayyana cewa sun kwashe kwanaki da dama a Madina ba tare da sun samu damar shiga Rawdah ba, lamarin da ya jefa su cikin fargabar barin birnin zuwa Makkah ba tare da sun ziyarci wajen ba.

Haka kuma, sun koka kan cewa manhajar tana da sarƙaƙiya da kuma wahalar amfani.

To sai dai, wasu jami’ai sun bayyana cewa tsarin yana tafiya yadda ya kamata matuƙar an bi ƙa’idojin da aka shimfiɗa.

Muhammad Aliyu, ɗaya daga cikin jami’an Amirul Hajj, ya tabbatar da cewa ya samu nasarar yin rajista ta manhajar, har ma ya taimaka wa wasu maniyyatan wajen ganin sun samu damar shiga.

A gefe guda kuma, wasu maniyyatan sun samu nasarar shiga Rawdah ta wasu ƙofofi daban bayan sun shafe lokaci suna jira, duk da cewa hakan ba ya cikin tsarin da hukuma ta amince da shi.

Rahotanni sun nuna cewa ƙarancin faɗakarwa da rashin horar da maniyyata kan yadda ake amfani da sabbin fasahohi na ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka haddasa wannan tsaiko.

A halin yanzu, fargaba ta mamaye zukatan maniyyata da dama kan yiwuwar barin Madina ba tare da sun gudanar da ziyara a Rawdah ba, wadda ake ɗauka ɗaya daga cikin mafi muhimmancin wurare a Musulunci.

MASU ALAKA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
Manyan Labarai

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Manufar Cire Haraji Za Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

Manufar Cire Haraji Za Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.