Rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi ta kama wasu mutane biyu bisa zargin su da haɗa kai wajen sace wata mota ƙirar Toyota Hilux mallakin shirin L-PRES.
A wata sanarwar da mai magana da yawun rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar a ranar Litinin, ya ce an kama waɗanda ake zargin ne bayan da aka shigar da ƙorafin ɓacewar motar a caji ofis ɗin ‘B’ Division a ranar 12 ga watan Disamba.
- ‘Yansanda Sun Fara Binciken Kisan Wani Ladanin Masallaci A Kano
- APC Ta Ƙaryata Zargin Hannun Matawalle A Haddasa Ta’addanci
A cewar sanarwar, wani mai suna Ibrahim A. Markus, mai kula da harkokin tsaro na kamfanin ‘Royal Security Guard Limited’ kuma mazaunin unguwar Wuntin Dada, Bauchi, ya shaida wa ‘yansanda cewa wasu masu gadi su biyu da ke aiki a ofishin L-PRES da ke kan layin Adamu Jumba Road, GRA, Bauchi, ake zargi da haɗa baki wajen sace motar.
Mai shigar da ƙorafin ya bayyana cewar a ranar 11 ga watan Disamba bayan sun samu kiran waya daga Kodinetan hukumar da ke sanar da su ɓacewar motar.
Waɗanda ake zargin masu suna Yarda John, da ke GRA, Bauchi, da Jessy Danjuma, da ke unguwar State Low-Cost, Bauchi dukkanin masu shekaru 19 ne.
SP Nafiu Habib ya ƙara da cewa motar da aka sace mai launin fari ƙirar Toyota Hilux da ke ɗauke da lambar alamar 03B-04 BA, an kamota ne a layin Bauchi Club, da ke unguwar GRA, bayan baza neman motar da ‘yansanda suka yi.
Ya ci gaba da cewa waɗanda ake zargin su ma an kama su a lokacin da ‘yansandan suka baza aiki gadan-gadan kan rahoton sace motar da suka samu.
Mai magana da yawun rundunar ya tabbatar da cewa bincike na ci gaba da gudana kuma da zarar suka kammala za su gurfanar da waɗanda ake zargin a kotu domin fuskantar zargin da ake musu.
Rundunar ta tabbatar wa jama’a azamarta na ci gaba da zage damtse domin tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.














