ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Bisa Zargin Luwaɗi Da Ƙananan Yara A Bauchi 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Yansanda

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta cafke wasu matasa guda biyu bisa zarginsu da cin zarafin wasu ƙananan yara ta hanyar tursasawa wajen yin Luwaɗi da su a Tilden Fulani da ke ƙaramar hukumar Toro ta jihar.

 

A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, SP Nafiu Habib, ya fitar a jiya, wani mahaifin da lamarin ya tada wa hankali ne ya kai rahoton faruwar lamarin a ranar 8 ga Janairu, 2026, zuwa ga shalkwatar ‘yansanda da ke Tilden Fulani.

ADVERTISEMENT
  • Duk Da Rashin Nasara A Hannun Morocco, BUA Ya Bai Wa Super Eagles Kyautar Dala 500,000
  • Sabuwar Yarjejeniyar FGN-ASUU: Tinubu Ya Amince Da Ƙarin Sabon Alawus Ga Farfesoshi

Mai ƙorafin ya yi zargin cewa wani matashi mai shekaru 16, mai suna Mohammed Saifullahi (wanda ake zargi) shi ne ya yaudari ɗansa mai shekaru 8 (an ɓoye sunansa) har ya yi masa Luwaɗi da ƙarfin tsiya.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A cewarsa, Saifullahi ya yi amfani a lokuta da dama da alewa da aya wajen janyo hankalin yaron domin ya yaudari shi don samun damar yin Luwaɗi da shi, lamarin da ya sanya ake zargin Saifullahi da cin zarafin yaron.

 

SP Habib ya ce bayan karɓar rahoton, nan take aka tura jami’an bincike zuwa yankin. An kama wanda ake zargi, yayin da aka garzaya da yaron da abin ya shafa zuwa asibiti domin duba lafiyarsa da kula da shi.

 

Ya ƙara da cewa, yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa cewa ya shafe sama da shekaru uku yana aikata irin wannan ɗanyen aikin na Luwadi, kuma ya ayyana sunan wani matashin Shuaibu Sulaiman, mai shekaru 17 a matsayin abokin cin burminsa.

 

A cewar sanarwar ‘yansandan zuwa yanzu dukkanin waɗanda ake zargin mutum biyun Saifullahi da Sulaiman duk suna tsare a hannun ‘yansanda.

 

Binciken farko na ‘yansanda (POI) ya kuma gano cewa wanda ake zargi na farko ya taɓa cin zarafin ƙananan yara huɗu masu shekaru tsakanin 7 zuwa 10.

 

“Saboda haka, duk mutanen da aka kama sun amsa laifinsu,” in ji kakakin ’yan sandan, yana mai ƙara da cewa bincike na ci gaba da gudana. Ya ce za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

 

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yi Allah-wadai da wannan aiki tare da gargaɗin cewa rundunar ba za ta lamunci kowace irin cin zarafi ga yara ba.

 

Ya kuma shawarci iyaye da masu kula da yara da su kasance masu sa ido sosai tare da lura da harkoki da motsin ’ya’yansu domin hana aukuwar irin waɗannan abubuwan a nan gaba.

Yansanda
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Yansanda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Zargin Almundahanar ₦1.35bn: Kotun Ƙoli Za Ta Warware Taƙaddamar EFCC Da Lamiɗo

Zargin Almundahanar ₦1.35bn: Kotun Ƙoli Za Ta Warware Taƙaddamar EFCC Da Lamiɗo

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.