ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Ceto Matafiya 76 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Kaduna

by Sadiq
4 years ago
Matafiya

Rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna ta ce ta ceto matafiya 76 da aka yi garkuwa da su a hanyar Funtua zuwa Zaria a unguwar Gulbala a karamar hukumar Giwa ta jihar, ta hanyar hadin gwiwa da sojoji.

Kakakin rundunar ‘yansandan, DSP Mohammed Jalige, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce an ceto mutanen ne a ranar Juma’a, bayan rahoton da aka samu daga hedikwatar ‘yansanda a karamar hukumar Giwa.

  • Xi Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Ilimi Karo Na 16 Na Cibiyoyin Kimiya Na Kasashe Masu Tasowa
  • Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Taron MDD Da Sin Kan Huldar Kasa Da Kasa Game Da Binciken Sararin Samaniya

A cewarsa, rundunar ‘yansandan ta samu rahoton ‘yan bindiga da dama ne suka tare hanya, kuma a cikin haka ne suka yi awon gaba da fasinjoji da dama, zuwa inda suke.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa, rundunar ta tattara jami’an tsaro ciki har da sojoji, inda suka shiga wurin, inda suka gano wata motar da babu kowa a ciki – wata motar kirar Ford mai dauke da lamba APP 667 XG, ta ce ta dauki fasinjojin da aka yi garkuwa da su.

Rundunar ta ce sojojin sun kara tarwatsa duk wani shingen hanya, tare da yin artabu da ‘yan bindigar tare da samun nasarar ceto dukkan mutane 76 da lamarin ya rutsa da su.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wadanda abin ya rutsa da su a cikin motar sun fito ne daga karamar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato zuwa wurare daban-daban, yayin da barayin suka tare su,” in ji shi.

A cewarsa, jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da aiki a yankin gaba daya domin neman babban direban babbar motar dakon kaya da wasu fasinjoji biyu da har yanzu ba a kai ga tantance su ba.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Yekini Ayoku, wanda ya bayyana jin dadinsa kan hadin kai tsakanin jami’an tsaro a jihar, ya alakanta wannan nasarar da kokarin da ‘yansanda da sojoji suka yi, kamar yadda ya ba jama’a tabbacin ci gaba da samun nasara a kan ‘yan bindiga da sauran masu aikata laifuka a jihar.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
2023: Takarar Peter Obi Za Ta Bai Wa PDP Matsala A Lokacin Zabe – Ganduje 

2023: Takarar Peter Obi Za Ta Bai Wa PDP Matsala A Lokacin Zabe - Ganduje 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.