Rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta ce ta kama mutane 244 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar a watan Agusta.
Kwamishinan ‘Yansandan jihar, Ibrahim Bakori ne, ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a hedikwatar rundunar da ke Bompai, Kano.
Bakori ya ce waɗanda aka kama sun haɗa da mutane takwas da ake zargi da garkuwa da mutane, 28 da ake zargi da fashi da makami, bakwai da ake zargi da satar motoci, 19 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, 117 da ake zargi da faɗan daba da kuma wasu mutane 65 da ake zargi da aikata wasu manyan laifuka.
Ya ce an gudanar da kamen ne ta hanyar amfani da bayanan sirri, samamen wuraren da ake zargin masu aikata laifuka na fakewa, sintiri na sa’o’i 24, binciken ababen hawa da mutane da kuma haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da shugabannin al’umma.
Kwamishinan ya ce jami’an rundunar sun kuma ƙwato ɗimbin miyagun ƙwayoyi a yayin samamen.
Daga cikin abubuwan da aka ƙwato akwai sachet 17,070 da kwalaye biyar na Tramadol, sachet 49, kwalaye uku da fakiti 18 na Diazepam, sachet 90 na Pregabalin, ƙwayoyin Exol guda 210 da kuma tabar wiwi guda 614.
Bakori ya kuma ce rundunar ta ƙwato bindigogi ƙirar pistol guda uku da harsasai guda 65 da aka su dangantawa da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba.
Ya ce an kuma ƙwato motoci guda shida, babura masu kafa uku guda huɗu da kuma babura guda bakwai da ake zargin ƙungiyoyin masu aikata laifuka sun mallaka ko suka yi amfani da su.
A cewarsa, ayyukan rundunar sun taimaka wajen rage manyan laifuka tare da inganta tsaro a wasu yankunan birnin Kano da a baya ake kallonsu a matsayin wuraren da ake yawan samun matsalar tsaro.
Ya bayyana Dala, Kofar Nassarawa, Sheka, Dorayi, Rimin Kebbe da Hotoro a matsayin wasu daga cikin wuraren da aka samu ingantaccen tsaro.
Sai dai Bakori ya ce rundunar na ƙara tsaurara ayyukanta a Bachirawa, Gobirawa da Tudun Fulani domin kawo ƙarshen ragowar ƙungiyoyin daba da ke ci gaba da aiki a yankunan.
Ya yi kira ga mazauna jihar da su ci gaba da bai wa ‘yansanda sahihan bayanai kan ayyukan masu aikata laifuka a cikin yankunansu.
Kwamishinan ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa rundunar za ta ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Bakori ya kuma bayyana cewa rundunar ta fara shirye-shiryen tsaro domin tunkarar gangamin siyasa da babban zaɓen shekarar 2027.
Ya gargaɗi ‘yan siyasa da magoya bayansu da su guji kalaman ƙiyayya, tashin hankali da daba, yana mai cewa rundunar ba za ta bari irin waɗannan ayyuka su kawo cikas ga zaman lafiya a jihar ba.














