Wata gobara ta tashi a ranar Lahadi a Terminal 2 na Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Murtala Muhammed da ke Legas, lamarin da ya sa Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN) ta gaggauta tura jami’an kashe gobara zuwa wurin.
FAAN ta tabbatar da faruwar lamarin ne cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na hukuma na X, inda ta ce jami’an Sashen Ceto da Kashe Gobara na Filin Jirgin Sama (ARFFS) sun isa wurin domin shawo kan gobarar.
A cewar hukumar, jami’an kashe gobarar na ci gaba da aiki domin kashe wutar.
FAAN ta kuma tabbatar wa jama’a cewa zuwa lokacin fitar da wannan rahoto, ba a samu asarar rayuka ko jikkatar kowa ba sakamakon gobarar.
Sai dai har yanzu ba a bayyana musabbabin tashin gobarar ba, kuma ba a tabbatar ko lamarin ya shafi zirga-zirgar jiragen sama da ayyukan filin jirgin ba.














