ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya? (3)

by Sulaiman
7 months ago
ASUU

….ci gaba daga makon da ya gabata

Bayan waɗannan jerin yajin aikin da kungiyar ta aiwatar, ASUU ta kuma tsunduma wani yajin aikin gargaɗi na makonni biyu a ranar 13 ga watan Oktoban 2025 sannan bayan haka, ta bai wa gwamnatin mako guda don biyan buƙatunta.

 

ADVERTISEMENT

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Chris Piwuna, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai da suka gudanar a cibiyar ASUU da ke Jami’ar Abuja, inda ya zargi Gwamnatin Tarayya da nuna halin ko in kula da buƙatun ƙungiyar.

  • Muhimman Abubuwa 5 Game Da Kasafin Kuɗin 2026 Da Gwamna Raɗɗa Ya Sanya Wa Hannu
  • Amfanin Zogale Ga Lafiyar Jikin Ɗan’adam

Piwuna, ya ce gwamnati ta gaza cika alƙawurran da ta ɗauka duk da sanarwar kwanaki 14 da ASUU ta bayar tun a ranar 28 ga Satumba, 2025.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

 

A yunƙurin biyan buƙatun ƙungiyar, Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

 

Tattaunawar Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Ma’aikatan Jami’o’i (ASUU) ta kara zurfafa, inda aka fara sakin Naira biliyan 2.3 ga jami’o’i a fadin kasar a matsayin wani bangare na kokarin magance matsalolin jin dadi da walwalar Malamai a fannin ilimin manyan makarantu.

 

Ministan Ilimi, Dr. Maruf Olatunji Alausa, ya bayyana cewa, Naira biliyan 2.311 da aka fara fitarwa, yana matsayin albashin rukuni na 8 ne da kuma basussukan kudin karin girma ga ma’aikatan jami’a.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi, Folasade Boriowo ya fitar ranar Laraba a Abuja.

 

A wani ci gaba daga ɓangaren gwamnatin, an rahoto cewa, Shugaba Tinubu ya umarci Ma’aikatar Ilimi ta kawo ƙarshen uajin aikin ASUU

 

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ya ƙwanƙwashi Ma’aikatar Ilimi don tabbatar da cewa, ɗaliban jami’a suna ci gaba da karatunsu ba tare da wani cikas ba, yana mai cewa, Gwamnatin Tarayya tana yin duk abin da ya dace don hana Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) tsunduma wani yajin aiki a nan gaba.

 

Da yake magana da manema labarai na Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja, a ranar Talata, 4 ga watan Nuwamban 2025, Ministan ya ce Shugaba Tinubu ya umarce shi da ya nemo mafita mai ɗorewa ga duk wata matsala da ka iya kawo cikas ga ayyukan ilimi a manyan makarantun ƙasar nan.

 

A ci gaba da tattaunawa domin samar da walwala da jin dadin Malaman jami’o’i, gwamnatin tarayya ta yi wa ASUU ta yin karin albashi da kashi 35 amma kungiyar ta yi watsi da wannan tayin inda ta bukaci gwamnatin ta kara hoɓɓasa.

 

Ta kuma bayyana cewa, har yanzu ba a magance muhimman matsalolin da ASUU ta daɗe tana kuka a kansu ba.

 

A wani hoɓɓasa da gwamnatin tarayya ta yi, ASUU ta yi nasarar cimma manyan buƙatunta na yarjejeniyar 2009 Da Gwamnati

 

ASUU ta fitar da wani rahoton nasarori da ta samu kan takaddamar yarjejeniyarta da gwamnatin tarayya ta 2009, inda ta samu sabbin alƙawurra kan ‘yancin kai na jami’o’i, kuɗaɗe, shugabanci, albashi da walwalar ma’aikata.

 

Kungiyar ta ce ɓangarorin biyu sun amince da cikakken ‘yancin kai, aiwatar da dokokin da ake da su kan Majalisar Gudanarwa, tabbatar da nadin mataimakin shugaban jami’a (VC) bisa cancanta da kuma ba da damar gudanar da zaɓuka na cikin gida don shugabancin sashe da malamai.

 

A cikin wata sanarwar manema labarai, da shugaban kungiyar Christopher Piwuna ya sanya wa hannu, ta amince cewa, karatuttukan kafin digiri za su takaita ne ga fannonin kimiyya, kuma yanzu za a riƙa yin ƙarin girma ne bisa ga sakamakon binciken da malami ke yi. Za kuma a cire wa jami’o’i harajin shigo da kayayyakin karatu.

 

Kwamitin aiwatarwa da sashin sa ido na NUC zai kula da aiwatar da wannan yarjejeniyar, tare da yin bita a duk bayan shekaru uku. ASUU ta amince da tsarin albashi da aka gyara wanda ya yi daidai da shawarar Nimi Briggs, yayin da za a biya alawus-alawus da aka samu kowace shekara a kashi 12% na kudin albashin kowace jami’a. An kuma amince da wani sashe na rashin cin zarafin malamai.

 

Wannan sanarwar ta fito ne daga shafin sada zumunta na kungiyar a ranar Talata, 2 ga Disamba, 2025 da tsakar rana.

 

Daga ƙarshe, muna fata gwamnati ta cika sabbin alƙawurran da ta ɗaukarwa kungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa don kaucewa barazanar wani sabon yajin aikin.

Asuu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Asuu

An Jinjina Wa Shugaban NPA Kan Rage Cunkoso A Tashar Apapa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.