ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 5 Game Da Kasafin Kuɗin 2026 Da Gwamna Raɗɗa Ya Sanya Wa Hannu

by El-Zaharadeen Umar
7 months ago
Abubuwa

A cikin makon nan ne, gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya sanya hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2026 na kimanin naira miliyan 897,000,000:00, inda ya zama doka domin fara aiwatar da shi.

Kasafin kuɗin da aka yi wa take da cewa “Kasafin Kudin da Jama’a Suka Tsara da Kansu” ta hanyar jin irin buƙatunsu wanda ita kuma gwamnati za ta aiwatar bisa doka.

  • Gobara Ta Yi Ajalin Mutum 5 ‘Yan Gida Ɗaya A Jihar Katsina
  • Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 

A iya cewa Gwamna Raɗɗa yana daga cikin gwamnonin arewacin Nijeriya da suka zama na farko da suka gabatar da kasafin kuɗn shekarar 2026, sannan aka kammala kare kasafin kudin a cikin kwanaki 24 na aikin a gaban zauren majalisa.

ADVERTISEMENT

A wannan kasafin kuɗin, akwai abubuwan da yawa da suka sha bamban da sauran kasafin kuɗaɗen da aka saba aiwatar a gwamnatance, musamman a Jiha Katsina da take da ƙarancin samun kuɗaɗen shiga.

Yana da kyau al’umma su gane cewa gwamnatoci na aiwatar da kasafin kuɗin yadda suka ga dama kuma yadda suke so, saboda doka ta ba su damar haka, sai dai wani abin da ba a saba gani ba shi ne, bai wa jama’a dama su bayyana abubuwan da suke so gwamnati ta yi masu.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Abu na farko da za a duba a cikin wannan kasafin kuɗi har na naira biliyan 897,865,078,282.05 wanda gwamnatin ta dage cewa jama’a ne da kansu suka shirya shi kuma suke san gwamnati ta aiwatar masu da shi.

Wannan shi ne kasafin kudi mafi girma da yawa a tarihin Jihar Katsina, kuma idan ta tabbata cewa na jama’a ne an yi bisa abin da jama’a suke so, to lallai abubuwa da yawa za su canza ta fuskar tattalin arziki da ci gaban al’umma da sauran ɓangarori.

Abu na biyu kan wannan kasafin kuɗi shi ne, zargin da ake yi wa sauran gwamnoni shi ma Malam Raɗɗa bai wuce shi ba, domin ana zargin cewa shekarar zaɓe ta zo za su yi amfani da wannan damar wajen samarwa da kan su kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe.

Abu na uku shi ne, gaba ɗaya kasafin kuɗin na naira biliyan 897,865.000 kashi 18 ne kaɗai zai tafi wajen harkokin gudanarwa kuma shi ne mafi ƙarancin da aka taɓa yi a tarihin Jihar Katsina.

Haka kuma wani sabon tarihin da za a sake kafawa shi ne, kashi 81 na kasafin kuɗin zai tafi ne a manyan ayyuka da gwamnatin Jihar Katsina ta ce jama’a ne da kan su suka zaɓi a yi masu haka.

Abu na huɗu shi ne, har zuwa yanzu babu gundarin kasafin kuɗin a hannun jama’a balanta a ga irin buƙatun da aka fi so da kuma begen a yi a wannan jiha da kowa ya yi imanin cewa kawar da matsalar tsaro ita ce baban abin da jama’a suka fi so a yi masu.

Idan aka duba daftarin kasafin kuɗin 2026 za a ga cewa ba a bai wa ɓangaren tsaro wani kaso mai tsoka ba duk da cewa idan harka ta shafi tsaro ana ƙoƙarin ɓoye ta, saboda harkar tsaro harka ce ta gwamnati kawai.

Abin da masana ke cewa shi ne, idan har babu tsaro duk waɗancan abubuwa da aka lissafa su, ba za su samu ba sai da tsaro, to amma an ce al’umma ta zaɓi wani abu fiye da tsaro da ya raba su da gidajansu da iyalansu da dukiyoyinsu.

Abu na ƙarshe shi ne, Gwamna Raɗɗa ya tabbatar wa jama’a cewa aiwatar da kasafin 2026 zai kasance cikin lokaci, a fili, kuma bisa buƙatunsu. Ya ƙara tabbatar da samar da ci gaba a fannin tsaro a Katsina domin samar da zaman lafiya.

A iya cewa wannan ikirarin da gwamnatin Malam Raɗɗa ta yi shi zai zame mata zakaran gwajin dafi da zai jagoranci samun nasarar gwamnatinsa ko akasin haka.?

Abubuwa
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Next Post
Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya

Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.