ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 5 Game Da Kasafin Kuɗin 2026 Da Gwamna Raɗɗa Ya Sanya Wa Hannu

by El-Zaharadeen Umar
9 months ago
Abubuwa

A cikin makon nan ne, gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya sanya hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2026 na kimanin naira miliyan 897,000,000:00, inda ya zama doka domin fara aiwatar da shi.

Kasafin kuɗin da aka yi wa take da cewa “Kasafin Kudin da Jama’a Suka Tsara da Kansu” ta hanyar jin irin buƙatunsu wanda ita kuma gwamnati za ta aiwatar bisa doka.

  • Gobara Ta Yi Ajalin Mutum 5 ‘Yan Gida Ɗaya A Jihar Katsina
  • Gwamnatin Katsina Da UNICEF Za Su Yi Wa Yara Miliyan 2.8 Allurar rigakafi A Katsina 

A iya cewa Gwamna Raɗɗa yana daga cikin gwamnonin arewacin Nijeriya da suka zama na farko da suka gabatar da kasafin kuɗn shekarar 2026, sannan aka kammala kare kasafin kudin a cikin kwanaki 24 na aikin a gaban zauren majalisa.

ADVERTISEMENT

A wannan kasafin kuɗin, akwai abubuwan da yawa da suka sha bamban da sauran kasafin kuɗaɗen da aka saba aiwatar a gwamnatance, musamman a Jiha Katsina da take da ƙarancin samun kuɗaɗen shiga.

Yana da kyau al’umma su gane cewa gwamnatoci na aiwatar da kasafin kuɗin yadda suka ga dama kuma yadda suke so, saboda doka ta ba su damar haka, sai dai wani abin da ba a saba gani ba shi ne, bai wa jama’a dama su bayyana abubuwan da suke so gwamnati ta yi masu.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Abu na farko da za a duba a cikin wannan kasafin kuɗi har na naira biliyan 897,865,078,282.05 wanda gwamnatin ta dage cewa jama’a ne da kansu suka shirya shi kuma suke san gwamnati ta aiwatar masu da shi.

Wannan shi ne kasafin kudi mafi girma da yawa a tarihin Jihar Katsina, kuma idan ta tabbata cewa na jama’a ne an yi bisa abin da jama’a suke so, to lallai abubuwa da yawa za su canza ta fuskar tattalin arziki da ci gaban al’umma da sauran ɓangarori.

Abu na biyu kan wannan kasafin kuɗi shi ne, zargin da ake yi wa sauran gwamnoni shi ma Malam Raɗɗa bai wuce shi ba, domin ana zargin cewa shekarar zaɓe ta zo za su yi amfani da wannan damar wajen samarwa da kan su kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe.

Abu na uku shi ne, gaba ɗaya kasafin kuɗin na naira biliyan 897,865.000 kashi 18 ne kaɗai zai tafi wajen harkokin gudanarwa kuma shi ne mafi ƙarancin da aka taɓa yi a tarihin Jihar Katsina.

Haka kuma wani sabon tarihin da za a sake kafawa shi ne, kashi 81 na kasafin kuɗin zai tafi ne a manyan ayyuka da gwamnatin Jihar Katsina ta ce jama’a ne da kan su suka zaɓi a yi masu haka.

Abu na huɗu shi ne, har zuwa yanzu babu gundarin kasafin kuɗin a hannun jama’a balanta a ga irin buƙatun da aka fi so da kuma begen a yi a wannan jiha da kowa ya yi imanin cewa kawar da matsalar tsaro ita ce baban abin da jama’a suka fi so a yi masu.

Idan aka duba daftarin kasafin kuɗin 2026 za a ga cewa ba a bai wa ɓangaren tsaro wani kaso mai tsoka ba duk da cewa idan harka ta shafi tsaro ana ƙoƙarin ɓoye ta, saboda harkar tsaro harka ce ta gwamnati kawai.

Abin da masana ke cewa shi ne, idan har babu tsaro duk waɗancan abubuwa da aka lissafa su, ba za su samu ba sai da tsaro, to amma an ce al’umma ta zaɓi wani abu fiye da tsaro da ya raba su da gidajansu da iyalansu da dukiyoyinsu.

Abu na ƙarshe shi ne, Gwamna Raɗɗa ya tabbatar wa jama’a cewa aiwatar da kasafin 2026 zai kasance cikin lokaci, a fili, kuma bisa buƙatunsu. Ya ƙara tabbatar da samar da ci gaba a fannin tsaro a Katsina domin samar da zaman lafiya.

A iya cewa wannan ikirarin da gwamnatin Malam Raɗɗa ta yi shi zai zame mata zakaran gwajin dafi da zai jagoranci samun nasarar gwamnatinsa ko akasin haka.?

Abubuwa
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya

Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.