ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunƙurin Tinubu Na Mayar Da Kano Jiha Mai Jam’iyya Ɗaya Zai Ci Tura — Tanko Yakasai

by Muhammad Bashir
5 months ago
Tanko Yakasai

Wani ɗan siyasa kuma tsohon ɗan takarar Jam’iyyar PRP a zaɓen 2023, Salihu Tanko Yakasai, ya zargi Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da yunƙurin amfani da dabarun siyasa wajen mayar da Jihar Kano jiha mai jam’iyya ɗaya, yana mai cewa wannan tunani kuskure ne mai girma.

Yakasai, wanda shi ne tsohon mai taimaka wa tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, a ɓangaren yaɗa labarai, ya ajiye mukaminsa kwanan nan tare da ficewa daga Jam’iyyar APC, inda ya koma Jam’iyyar ADC, sakamakon rashin gamsuwa da yadda ya ce ake tafiyar da mulki a ƙarƙashin shugabancin Tinubu.

  • Harin Filato: JNI Ta Tabbatar Da Kashe Mambobinta 4, 10 Sun Ɓace
  • Farfadowar Halittun Ruwa A Kogin Yangtze Ta Nuna Kyakkyawan Yanayi

A cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar 1 ga Afrilu, 2026, Yakasai ya ce tarihin siyasar Kano ya nuna cewa tun daga zamanin jam’iyyar Northern Elements Progressive Union (NEPU) har zuwa lokutan “Santsi da Tabo”, jihar ba ta taɓa zama ƙarƙashin jam’iyya ɗaya ba, kuma hakan ba zai sauya ba. Ya ƙara da cewa, “Kano ba Lagos ba ce,” yana mai nuni da bambancin tsarin siyasa tsakanin jihohin biyu.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa siyasar Kano ta ginu ne kan kishin al’umma, gaskiya da tsayawa kan akida, wadda marigayi Aminu Kano ya shimfiɗa. A cewarsa, adawa a Kano ba don adawa kawai ake yi ba, sai don tabbatar da ci gaban al’umma, ingantaccen shugabanci, adalci da riƙon amana.

Yakasai ya kuma nuna damuwa kan abin da ya kira watsi da korafe-korafen al’ummar Kano, musamman dangane da zargin karkatar da muƙaman gwamnati da kuma fifita wasu yankuna a ayyukan ci gaba. Ya ce irin wannan hali ba zai haifar da goyon bayan jama’a ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Ya jaddada cewa biyayya ga shugabanci tana samuwa ne ta hanyar adalci da kyautatawa, ba ta hanyar tilastawa ko amfani da dabarun siyasa da yaudara ba.

A ƙarshe, ya ce idan aka ci gaba da abin da ya kira hana Kano haƙƙinta, al’ummar jihar za su mayar da martani ne ta akwatin zaɓe, yana mai cewa wannan ita ce hanya mafi sauƙi kuma mafi dacewa a tsarin dimokuraɗiyya.

Ya rufe da kalmar, “Falle ɗaya ce (F1).”

Tanko Yakasai
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Tanko Yakasai
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta Bana

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.