ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunƙurin Tinubu Na Mayar Da Kano Jiha Mai Jam’iyya Ɗaya Zai Ci Tura — Tanko Yakasai

by Muhammad Bashir
2 months ago
Tanko Yakasai

Wani ɗan siyasa kuma tsohon ɗan takarar Jam’iyyar PRP a zaɓen 2023, Salihu Tanko Yakasai, ya zargi Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da yunƙurin amfani da dabarun siyasa wajen mayar da Jihar Kano jiha mai jam’iyya ɗaya, yana mai cewa wannan tunani kuskure ne mai girma.

Yakasai, wanda shi ne tsohon mai taimaka wa tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, a ɓangaren yaɗa labarai, ya ajiye mukaminsa kwanan nan tare da ficewa daga Jam’iyyar APC, inda ya koma Jam’iyyar ADC, sakamakon rashin gamsuwa da yadda ya ce ake tafiyar da mulki a ƙarƙashin shugabancin Tinubu.

  • Harin Filato: JNI Ta Tabbatar Da Kashe Mambobinta 4, 10 Sun Ɓace
  • Farfadowar Halittun Ruwa A Kogin Yangtze Ta Nuna Kyakkyawan Yanayi

A cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar 1 ga Afrilu, 2026, Yakasai ya ce tarihin siyasar Kano ya nuna cewa tun daga zamanin jam’iyyar Northern Elements Progressive Union (NEPU) har zuwa lokutan “Santsi da Tabo”, jihar ba ta taɓa zama ƙarƙashin jam’iyya ɗaya ba, kuma hakan ba zai sauya ba. Ya ƙara da cewa, “Kano ba Lagos ba ce,” yana mai nuni da bambancin tsarin siyasa tsakanin jihohin biyu.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa siyasar Kano ta ginu ne kan kishin al’umma, gaskiya da tsayawa kan akida, wadda marigayi Aminu Kano ya shimfiɗa. A cewarsa, adawa a Kano ba don adawa kawai ake yi ba, sai don tabbatar da ci gaban al’umma, ingantaccen shugabanci, adalci da riƙon amana.

Yakasai ya kuma nuna damuwa kan abin da ya kira watsi da korafe-korafen al’ummar Kano, musamman dangane da zargin karkatar da muƙaman gwamnati da kuma fifita wasu yankuna a ayyukan ci gaba. Ya ce irin wannan hali ba zai haifar da goyon bayan jama’a ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ya jaddada cewa biyayya ga shugabanci tana samuwa ne ta hanyar adalci da kyautatawa, ba ta hanyar tilastawa ko amfani da dabarun siyasa da yaudara ba.

A ƙarshe, ya ce idan aka ci gaba da abin da ya kira hana Kano haƙƙinta, al’ummar jihar za su mayar da martani ne ta akwatin zaɓe, yana mai cewa wannan ita ce hanya mafi sauƙi kuma mafi dacewa a tsarin dimokuraɗiyya.

Ya rufe da kalmar, “Falle ɗaya ce (F1).”

Tanko Yakasai
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta Bana

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta Bana

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.