Wani jigo a jam’iyyar ADC, Buba Galadima, ya yi zargin cewa jam’iyyun adawa na iya fuskantar takura a harkokin siyasa gabanin zaɓen 2027, yana mai gargaɗin cewa jam’iyyar APC mai mulki na iya hana ADC gudanar da kamfe.
Galadima, ya bayyana hakan ne a ranar Talata, a Abuja, yayin taron ƙasa na jam’iyar ADC, inda ya soki Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, yana mai cewa shugaban zai sha kaye a zaɓen 2027 ko ta halin ƙaƙa.
Rashin Tsaro: Ba Wani Abun Mamaki Idan ‘Yan Bindiga Suka Sace Buhari – Buba Galadima
Atiku Na Tura Manyan Mutane Su Roki Kwankwaso Ya Mara Wa Takararsa Baya – Buba Galadima
Ya yabawa ADC bisa ci gaba da gudanar da taronta duk da abin da ya kira “barazana da tsoratarwa,” yana mai zargin cewa an yi ƙoƙarin tarwatsa taron ta hanyar matsin lamba ga shugaban taron.
Har ila yau Buba Galadima, ya zargi gwamnatin APC da ƙoƙarin raunana jam’iyyun adawa da dama, ciki har da PDP, da SDP, da kuma NNPP, har ma da jam’iyyarsu.
Ya kuma buƙaci ‘yan siyasa da magoya baya da su ƙi amincewa da abin da ya kira yunƙurin ƙuntata siyasar adawa a ƙasarnan, yana mai jaddada cewa juriya da ƙarfin hali su ne mabuɗin kayar da jam’iyya mai mulki a zaɓen 2027 da ke tafe.















Discussion about this post