Rundunar Sojin Nijeriya ta samu gagarumar nasara a yaƙin da take yi da ‘yan bindiga a jihar Bauchi, bayan gudanar da hare-haren tsaftace dazuka da suka kai ga lalata sansanonin ‘yan bindiga da kama wasu daga cikin iyalansu.
A wata sanarwa da rundunar ta wallafa, ta ce dakarun Brigadiya ta 33 tare da haɗin gwuiwar ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro sun kai sumame a Dajin Madam, inda suka tarwatsa sansanonin Azuge da Hari da ake zargi da zama mafakar masu laifi.
Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurkaz ‘Yan Bindiga
Diezani Ta Kashe Fam 140,000 A Kayan Daki Masu Tsada – Kotun Birtaniya
Sanarwar ta ce an hallaka wasu daga cikin ‘yan bindigar yayin da wasu suka tsere sakamakon matsin lamba daga sojoji, inda aka kama iyalansu guda 19, ciki har da mata shida da yara 13.
Haka kuma, an lalata babura da dama da ‘yan bindigar ke amfani da su wajen kai hare-hare, tare da kwato kayayyaki kamar harsashin AK-47, da kwayoyin tramadol, da kayan sojoji da na ‘yan sanda, da kuma dawaki biyu.
Rundunar ta ce dakarunta na ci gaba da zama a yankin domin hana sake dawowar ‘yan bindigar, tana mai jaddada ƙudurinta na ci gaba da murƙushe duk wani nau’in ta’addanci tare da kira ga jama’a da su riƙa bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai.















Discussion about this post