ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Tuhumi Bukola Saraki Da Abdulfatai Ahmed Da Laifin Kisa

by Abubakar Sulaiman
2 months ago

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dr. Bukola Saraki, da tsohon gwamnan jihar Kwara, Abdulfatai Ahmed, za su gurfana a gaban kotu a ranar 4 ga Yuni, 2026 domin fuskantar sabbin tuhume-tuhume guda 20 da suka haɗa da kisan kai, da haɗa baki da sauran laifuffuka dangane da fashin da aka yi a Offa a shekarar 2018.

An shigar da karar ne a gaban Mai Shari’a Haleemah Salman ta Babbar Kotun Jihar Kwara, inda kuma aka hada da Yusuf Abdulwahab da Alabi Olalekan a matsayin waɗanda ake kara.

Florence-Morenike-Saraki-and-Abubakar-Bukola-Saraki

ADVERTISEMENT

Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki

An ce ƙarar, mai lamba LWS/114C/26, an shigar da ita ne a ranar 9 ga Afrilu, 2026 daga hannun Babban Lauyan Jihar Kwara, Ibrahim Sulyman (SAN), kuma ana sa ran za a miƙa wa waɗanda ake ƙara takardun tuhuma a ranar Juma’a, 17 ga Afrilu, 2026. Wannan sabuwar shari’ar ta zuwa ne bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa manyan waɗanda suka aikata fashin, ciki har da Ayo Akinnibosun.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Masu gabatar da ƙara sun zargi waɗanda ake ƙara da haɗa baki wajen ɗaukar nauyi da kuma ba da makamai ga wasu da ake alaƙanta su da harin na Afrilu 2018 a Offa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da tayar da hankalin jama’a. An ce Akinnibosun, wanda aka riga aka yankewa hukunci, ya bayyana kansa a matsayin mai aikata kisan kai a ƙarƙashin wata alaƙa ta siyasa da ake dangantawa da waɗanda ake kara.

Haka kuma, ana zargin cewa ya karɓi bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu daga Yusuf Abdulwahab kafin wani taron siyasa, tare da karbar mota kirar Toyota Lexus mai dauke da lambar Saraki da kuma kudi da aka kira “tallafin siyasa”. Ana kuma cewa wasu daga cikin waɗanda aka yankewa hukunci sun raka Saraki yayin ziyarar jaje da ya kai Offa bayan harin, tare da gano wasu motoci da kayayyaki daga ofisoshin gwamnati a jihar Kwara da aka yi amfani da su a matsayin hujja.

Sai dai Saraki ya sha musanta hannu a lamarin, yana mai cewa zarge-zargen siyasa ce kawai da aka ƙirƙira domin ɓata masa suna. Shi ma Abdulfatai Ahmed ya ƙaryata zargin, yana mai cewa ba su da tushe. Ana sa ran shari’ar za ta jawo hankalin ƙasa baki ɗaya, yayin da ake shirin fara sauraron ƙarar a ranar 4 ga Yuni, 2026, kuma ana sa ran Saraki da jam’iyyar PDP a jihar Kwara za su mayar da martani nan ba da jimawa ba.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Tsinci Gawar Ministan Sadarwa Na Burundi A Cikin Motarsa

An Tsinci Gawar Ministan Sadarwa Na Burundi A Cikin Motarsa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.