ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Tuhumi Bukola Saraki Da Abdulfatai Ahmed Da Laifin Kisa

by Abubakar Sulaiman
2 months ago

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dr. Bukola Saraki, da tsohon gwamnan jihar Kwara, Abdulfatai Ahmed, za su gurfana a gaban kotu a ranar 4 ga Yuni, 2026 domin fuskantar sabbin tuhume-tuhume guda 20 da suka haɗa da kisan kai, da haɗa baki da sauran laifuffuka dangane da fashin da aka yi a Offa a shekarar 2018.

An shigar da karar ne a gaban Mai Shari’a Haleemah Salman ta Babbar Kotun Jihar Kwara, inda kuma aka hada da Yusuf Abdulwahab da Alabi Olalekan a matsayin waɗanda ake kara.

Florence-Morenike-Saraki-and-Abubakar-Bukola-Saraki

ADVERTISEMENT

Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki

An ce ƙarar, mai lamba LWS/114C/26, an shigar da ita ne a ranar 9 ga Afrilu, 2026 daga hannun Babban Lauyan Jihar Kwara, Ibrahim Sulyman (SAN), kuma ana sa ran za a miƙa wa waɗanda ake ƙara takardun tuhuma a ranar Juma’a, 17 ga Afrilu, 2026. Wannan sabuwar shari’ar ta zuwa ne bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa manyan waɗanda suka aikata fashin, ciki har da Ayo Akinnibosun.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Masu gabatar da ƙara sun zargi waɗanda ake ƙara da haɗa baki wajen ɗaukar nauyi da kuma ba da makamai ga wasu da ake alaƙanta su da harin na Afrilu 2018 a Offa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da tayar da hankalin jama’a. An ce Akinnibosun, wanda aka riga aka yankewa hukunci, ya bayyana kansa a matsayin mai aikata kisan kai a ƙarƙashin wata alaƙa ta siyasa da ake dangantawa da waɗanda ake kara.

Haka kuma, ana zargin cewa ya karɓi bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu daga Yusuf Abdulwahab kafin wani taron siyasa, tare da karbar mota kirar Toyota Lexus mai dauke da lambar Saraki da kuma kudi da aka kira “tallafin siyasa”. Ana kuma cewa wasu daga cikin waɗanda aka yankewa hukunci sun raka Saraki yayin ziyarar jaje da ya kai Offa bayan harin, tare da gano wasu motoci da kayayyaki daga ofisoshin gwamnati a jihar Kwara da aka yi amfani da su a matsayin hujja.

Sai dai Saraki ya sha musanta hannu a lamarin, yana mai cewa zarge-zargen siyasa ce kawai da aka ƙirƙira domin ɓata masa suna. Shi ma Abdulfatai Ahmed ya ƙaryata zargin, yana mai cewa ba su da tushe. Ana sa ran shari’ar za ta jawo hankalin ƙasa baki ɗaya, yayin da ake shirin fara sauraron ƙarar a ranar 4 ga Yuni, 2026, kuma ana sa ran Saraki da jam’iyyar PDP a jihar Kwara za su mayar da martani nan ba da jimawa ba.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
An Tsinci Gawar Ministan Sadarwa Na Burundi A Cikin Motarsa

An Tsinci Gawar Ministan Sadarwa Na Burundi A Cikin Motarsa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.