Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dr. Bukola Saraki, da tsohon gwamnan jihar Kwara, Abdulfatai Ahmed, za su gurfana a gaban kotu a ranar 4 ga Yuni, 2026 domin fuskantar sabbin tuhume-tuhume guda 20 da suka haɗa da kisan kai, da haɗa baki da sauran laifuffuka dangane da fashin da aka yi a Offa a shekarar 2018.
An shigar da karar ne a gaban Mai Shari’a Haleemah Salman ta Babbar Kotun Jihar Kwara, inda kuma aka hada da Yusuf Abdulwahab da Alabi Olalekan a matsayin waɗanda ake kara.
Florence-Morenike-Saraki-and-Abubakar-Bukola-Saraki
Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki
An ce ƙarar, mai lamba LWS/114C/26, an shigar da ita ne a ranar 9 ga Afrilu, 2026 daga hannun Babban Lauyan Jihar Kwara, Ibrahim Sulyman (SAN), kuma ana sa ran za a miƙa wa waɗanda ake ƙara takardun tuhuma a ranar Juma’a, 17 ga Afrilu, 2026. Wannan sabuwar shari’ar ta zuwa ne bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa manyan waɗanda suka aikata fashin, ciki har da Ayo Akinnibosun.
Masu gabatar da ƙara sun zargi waɗanda ake ƙara da haɗa baki wajen ɗaukar nauyi da kuma ba da makamai ga wasu da ake alaƙanta su da harin na Afrilu 2018 a Offa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da tayar da hankalin jama’a. An ce Akinnibosun, wanda aka riga aka yankewa hukunci, ya bayyana kansa a matsayin mai aikata kisan kai a ƙarƙashin wata alaƙa ta siyasa da ake dangantawa da waɗanda ake kara.
Haka kuma, ana zargin cewa ya karɓi bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu daga Yusuf Abdulwahab kafin wani taron siyasa, tare da karbar mota kirar Toyota Lexus mai dauke da lambar Saraki da kuma kudi da aka kira “tallafin siyasa”. Ana kuma cewa wasu daga cikin waɗanda aka yankewa hukunci sun raka Saraki yayin ziyarar jaje da ya kai Offa bayan harin, tare da gano wasu motoci da kayayyaki daga ofisoshin gwamnati a jihar Kwara da aka yi amfani da su a matsayin hujja.
Sai dai Saraki ya sha musanta hannu a lamarin, yana mai cewa zarge-zargen siyasa ce kawai da aka ƙirƙira domin ɓata masa suna. Shi ma Abdulfatai Ahmed ya ƙaryata zargin, yana mai cewa ba su da tushe. Ana sa ran shari’ar za ta jawo hankalin ƙasa baki ɗaya, yayin da ake shirin fara sauraron ƙarar a ranar 4 ga Yuni, 2026, kuma ana sa ran Saraki da jam’iyyar PDP a jihar Kwara za su mayar da martani nan ba da jimawa ba.















Discussion about this post