Ɗan takarar kujerar Ɗan Majalisar wakilai ta Tarayya a mazaɓar Kaduna ta Arewa ƙarƙashin Jam’iyyar (ADC), Honarabul Yazid Atta, ya bukaci al’ummar mazabar da su zabi shugabanni masu gaskiya da hangen nesa domin samar da ci gaba mai anfani ga jama’a.
Yazid Atta ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai inda ya bayyana kudurinsa na kawo sauyi da inganta rayuwar al’ummar mazabar idan aka ba shi dama a zaben da ke tafe.
Ɗan takarar ya ce ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da zai mayar da hankali a kai shi ne bunƙasa rayuwar matasa ta hanyar samar musu da ayyukan yi, horaswa da tallafawa harkokin kasuwanci.
A cewarsa, matasa da dama suna da basira da hazaka amma rashin dama da tallafi ne ke hana su cimma burinsu a rayuwa.
“Matasa su ne ginshikin kowace al’umma. Idan aka zaɓe ni, zan ƙirƙiro shirye-shiryen da za su taimaka wajen rage rashin aikin yi tare da ba matasa damar dogaro da kansu,” in ji shi.
Ya bayyana cewa, mazaɓar Kaduna ta Arewa na da ɗimbin damarmaki da ya kamata a amfana da su domin inganta rayuwar jama’a da bunkasa tattalin arziki.
Daga ƙarshe, ɗan takarar ya buƙaci masu kaɗa ƙuri’a da su guji siyasar yaudara tare da mara wa ‘yan takarar da suke da kishin talakawa baya.















Discussion about this post