A yau laraba ne aka gudanar da zanga -zangar lumana a babban birnin tarayyar Abuja kan hukuncin kotun koli na dakatar da CBN kan kudirinsa na daina amfani da tsoffin takardun kudi na Naira 200, 500, 1,000.
Masu zanga zangar da suka isa hedikwatar CBN da ofis din babban lauyan Gwamnati kuma ministan shari’a, sun nemi bankin kar ya goyi bayan hukuncin kotun.
A wasu rubuce-rubucen da suka yi a allunan zanga zangar ta su, sun kuma gargadi alkalin alkalai na kasa mai shari’a, Ariwoola ya gujewa mayar da kotun fagen rusa mulkin dimokuradiyya, sun kuma zarge shi da yiwa dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed aiki da kuma yan aware din gwamnonin PDP biyar.