Mataimakin Shugaban Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), VC, Farfesa Abdullahi Ibrahim Musa, ya musanta ikirarin reshen Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU-KASU) cewa sama da malamai 200 sun bar jami’ar saboda rashin aamun kyakkyawar kula daga gwamnatin jihar.
Jami’ar ta bayyana ikirarin a matsayin mai ruɗarwa kuma wanda bai yi daidai da halin da ake ciki a jami’ar ba.Wannan bayani ya biyo bayan wani taron manema labarai da ASUU-KASU ta gudanar kwanan nan, inda ƙungiyar ta bai wa Gwamnatin Jihar Kaduna wa’adin makonni biyu domin aiwatar da yarjejeniyar FGN-ASUU ta shekarar 2025, tare da magance wasu matsalolin jin daɗin ma’aikata.
A cikin wata sanarwa da Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Abdullahi Ibrahim Musa, ya fitar, mahukuntan KASU sun ce sauya wurin aiki da malaman jami’a da sauran ma’aikata ke yi tsakanin jami’o’i abu ne da ya zama ruwan dare a duniya, don haka bai kamata a ɗauke shi a matsayin hujjar rashin kyawun yanayin aiki a jami’ar ba.
Sanarwar ta ce sauyin ma’aikata ya zama ruwan dare a jami’o’i daban-daban, tare da jan hankalin ƙungiyar da kada ta danganta duk wani malami da ya bar jami’ar da matsalolin yanayin aiki.
Mahukuntan jami’ar sun kuma bukaci ASUU-KASU da ta gabatar da bayanai cikin gaskiya da adalci, tare da guje wa yada bayanan da za su iya haifar da fargaba ko damuwa ba tare da hujja ba.
Jami’ar ta ƙara da cewa nasarorin da KASU ta samu a baya-bayan nan na nuna cewa tana da yanayin karatu mai bunƙasa, tare da ƙarfafa matsayin jami’ar wajen jawo hankalin ƙwararrun malamai, riƙe su da kuma samar musu da kyakkyawan yanayin gudanar da bincike da koyarwa.














