Majalisar Dokokin Jihar Zamfara a ranar Laraba ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi biyu bisa zargin karkatar da kudaden gwamnati.
Shugabannin da abin ya shafa sun hada da Mannir Haidara na Karamar Hukumar Kaura Namoda da kuma Umar A. Faru na Karamar Hukumar Bukkuyum.
- Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris
- An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba
Dakatarwar ta biyo bayan amincewa da rahoton Kwamitin Majalisar kan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu, wanda aka gabatar yayin zaman majalisar.
Mai magana da yawun Majalisar, Bello Madaro Kurya, ya ce matakin na daga cikin kokarin kara inganta gaskiya da rikon amana a tafiyar da harkokin kananan hukumomi.
A cewarsa, kwamitin ya ba da shawarar dakatarwar ne bayan shugabannin sun gaza amsa gayyatar da aka yi musu domin su yi bayani kan yadda aka kashe kudaden da aka ware wa kananan hukumominsu.















Discussion about this post