ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
22 minutes ago
Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya ƙaddamar da rukunin gidaje 100, da gwamnatin Jihar Sakkwato da yi haɗin guiwa da Hukumar Raya Ƙasashe ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP) suka ginawa ƴan gudun hijira a Ƙaramar Hukumar Illela da ke Sakkwato.

A jawabinsa a wajen taron a wannan makon, Gwamna Zulum ya bayyana ayyukan a matsayin muhimmin matakin da zai kawar da matsalar muhalli tare da inganta jin daɗin al’umma da kuma ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa a Jihar Sakkwato.

Zulum ya yaba wa Hukumar Raya Ƙasashe ta UNDP da Gwamnatin Jamus da sauran abokan hulɗa na ci gaba kan ayyukan ci gaba da tallafi da suke bai wa Nijeriya, musamman a yankunan da rikice-rikice suka shafa. Ya ce irin waɗannan taimako sun taka muhimmiyar rawa wajen farfaɗowa da inganta rayuwar al’umma a faɗin ƙasar.

ADVERTISEMENT

Ya ce ire-iren ayyukan da hukumar ta aiwatar za su yi matuƙar tasiri ga al’ummar Jihar Sakkwato, musamman waɗanda ƴan ta’adda da ambaliya suka raba da muhallansu. Yana mai cewa matsalar tsaro a yankin arewa maso yamma ta haifar da ƙalubale da tarin matsaloli, wanda da ƙarfin soja kaɗai ba zai iya warware su ba.

Gwamna Zulum ya bayyana sabbin rukunin gidajen da aka ƙaddamar a matsayin muhimmin matakin da zai dawo da martaba da mutuncin waɗanda suka rasa matsugunansu, yayin da kasuwar ƙasa da ƙasa ta Illela, cibiyar zaman lafiya da sauyin yanayi da kuma aikin wutar lantarki na hasken rana za su ƙarfafawa al’umma da bunƙasa tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Tun da farko, Gwamna Ahmed Aliyu ya bayyana cewa an gina gidajen ne tare da haɗin guiwar UNDP domin samar da mafaka mai inganci ga mutanen da rikice-rikicen tsaro, ambaliya da sauran musibu suka raba da muhallansu.

Ya ce Jihar Sakkwato ta fuskanci mummunar ambaliya a shekarun 2024 da 2025, wadda ta shafi kusan ƙananan hukumomi 20 tare da tilasta wa mazauna da dama barin gidajensu musamman a Illela, inda iyalai da yawa suka tsinci kansu a sansanonin wucin-gadi da aka kafa a cikin makarantu.

Zulum
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Sulaiman
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Sulaiman
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Sulaiman
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Zulum
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ posts Bio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dimokuradiyyar Nijeriya A Shekara 27:Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

MASU ALAKA

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga
Labarai

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

June 20, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.