Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya ƙaddamar da rukunin gidaje 100, da gwamnatin Jihar Sakkwato da yi haɗin guiwa da Hukumar Raya Ƙasashe ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP) suka ginawa ƴan gudun hijira a Ƙaramar Hukumar Illela da ke Sakkwato.
A jawabinsa a wajen taron a wannan makon, Gwamna Zulum ya bayyana ayyukan a matsayin muhimmin matakin da zai kawar da matsalar muhalli tare da inganta jin daɗin al’umma da kuma ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa a Jihar Sakkwato.
Zulum ya yaba wa Hukumar Raya Ƙasashe ta UNDP da Gwamnatin Jamus da sauran abokan hulɗa na ci gaba kan ayyukan ci gaba da tallafi da suke bai wa Nijeriya, musamman a yankunan da rikice-rikice suka shafa. Ya ce irin waɗannan taimako sun taka muhimmiyar rawa wajen farfaɗowa da inganta rayuwar al’umma a faɗin ƙasar.
Ya ce ire-iren ayyukan da hukumar ta aiwatar za su yi matuƙar tasiri ga al’ummar Jihar Sakkwato, musamman waɗanda ƴan ta’adda da ambaliya suka raba da muhallansu. Yana mai cewa matsalar tsaro a yankin arewa maso yamma ta haifar da ƙalubale da tarin matsaloli, wanda da ƙarfin soja kaɗai ba zai iya warware su ba.
Gwamna Zulum ya bayyana sabbin rukunin gidajen da aka ƙaddamar a matsayin muhimmin matakin da zai dawo da martaba da mutuncin waɗanda suka rasa matsugunansu, yayin da kasuwar ƙasa da ƙasa ta Illela, cibiyar zaman lafiya da sauyin yanayi da kuma aikin wutar lantarki na hasken rana za su ƙarfafawa al’umma da bunƙasa tattalin arziki.
Tun da farko, Gwamna Ahmed Aliyu ya bayyana cewa an gina gidajen ne tare da haɗin guiwar UNDP domin samar da mafaka mai inganci ga mutanen da rikice-rikicen tsaro, ambaliya da sauran musibu suka raba da muhallansu.
Ya ce Jihar Sakkwato ta fuskanci mummunar ambaliya a shekarun 2024 da 2025, wadda ta shafi kusan ƙananan hukumomi 20 tare da tilasta wa mazauna da dama barin gidajensu musamman a Illela, inda iyalai da yawa suka tsinci kansu a sansanonin wucin-gadi da aka kafa a cikin makarantu.














Discussion about this post