A ƙalla ƙauyuka 17 da ke ƙaramar hukumar Faskari a Jihar Katsina ne suka fuskanci hare-haren ƴan bindiga tun daga ranar Juma’a, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wasu mazauna yankin tare da yin garkuwa da wasu.
Rahotanni sun ce hare-haren sun jefa al’ummomin yankin cikin fargaba, yayin da ƴan bindigar ke ci gaba da kai hare-hare tare da yin awon gaba da mazauna ƙauyukan.
Faskari na daga cikin ƙananan hukumomin Katsina da suka daɗe suna fama da matsalar ƴan bindiga, musamman hare-haren da suka shafi kisa, da garkuwa da mutane da tilasta wa mazauna barin gidajensu.
Hare-haren na baya-bayan nan sun ƙara nuna girman matsalar tsaro da ke addabar wasu al’ummomin jihar, inda mazauna yankunan karkara ke fuskantar barazanar rasa rayukansu da dukiyoyinsu.
Al’ummomin da abin ya shafa na ci gaba da fatan samun ƙarin matakan tsaro daga hukumomi domin daƙile hare-haren da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.














