Ƴan mata uku ƴan gida ɗaya sun mutu bayan kwale-kwalen da suke ciki ya kife a madatsar ruwan Tiga da ke Jihar Kano. Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da ‘yan matan ke tafiya a cikin kwale-kwalen, wanda daga bisani ya kife a cikin ruwan.
Rahoton daily trust ya bayyana cewa, mutuwar ‘yan uwan ukun ta jefa iyalansu da al’ummar yankin cikin jimami, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano cikakken bayani kan yadda haɗarin ya faru.
Haɗarin ya kuma sake jaddada buƙatar ƙara kula da tsaron masu amfani da kwale-kwale a madatsun ruwa da sauran wuraren da ake zirga-zirga ta ruwa.
Hukumomi na bukatar ƙara ɗaukar matakan kariya, musamman tabbatar da amfani da kayayyakin tsaro da kuma bin ƙa’idojin zirga-zirgar ta ruwa domin rage haɗurran kwale-kwale.














