Jami’an tsaron haɗin gwuiwa daga rundunar ƴansanda, DSS da Sojoji sun kuɓutar da mutane bakwai da aka yi garkuwa da su a jihar Kaduna, bayan wani sumame da aka kai kan sansanin masu garkuwa da mutane a dajin Kweri. Lamarin ya biyo bayan rahoton kai hare-haren da aka samu a unguwar Ushafa da ke karamar hukumar Bwari, Abuja, inda masu garkuwa suka kutsa cikin dare suka yi awon gaba da mazauna yankin.
Bayan samun kiran gaggawa a ranar 5 ga Disamba, tawagar jami’an tsaro ta bi sawun masu garkuwa da mayen bayanan sirri daga Mpape zuwa kananan garuruwan da ke hada Abuja da Kagarko a jihar Kaduna. Da suka hango jami’an tsaro, ‘yan ta’addan suka bude wuta, amma jami’an sun mayar da martani, abin da ya tilasta maharan barin mutum guda da suka sace yayin gudu. Bayan haka, jami’an tsaro suka ci gaba da bin sawunsu na tsawon sa’o’i bakwai a cikin duwatsu da dazuzzuka masu hatsari.
Binciken ya kai su har cikin dajin Kweri, inda aka sake artabun harbe-harbe mai tsanani da ya rushe karfin ‘yan bindigar, suka tsere suka bar sansaninsu. A yayin share wurin, an gano sauran mutane shida da aka yi garkuwa da su, lamarin da ya kai yawan wadanda aka kubutar zuwa bakwai gaba daya. An kaisu asibiti nan take, kuma ana tabbatar da suna samun kulawa cikin yanayi mai kyau.
Kakakin ƴansandan FCT, SP Josephine Adeh, ta ce an ƙara tsaurara matakan tsaro a yankunan da aka gano suna da haɗari domin daƙile sabbin hare-hare. Kwamishinan ƴansandan FCT, CP Miller Dantawaye, ya jinjinawa jajircewar jami’an, yana mai cewa kokari irin wannan na nuna kudirin gwamnati na karya karfin masu garkuwa da mutane a babbar birnin kasar.














