Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kama wani da ake zargi da safarar makamai tare da kwato bindigogi uku ƙirar AK-47 da aka ƙera a nan gida yayin wani sumame da ta kai a jihar.
Mai magana da yawun rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, inda ya ce jami’an sashin yaƙi da garkuwa da mutane ne suka gudanar da aikin a ranar Asabar, 9 ga Mayu, 2026, a unguwar Dandinshe da ke ƙaramar hukumar Dala.
A cewarsa, an gudanar da sumamen ne bisa umarnin kwamishinan ‘yansandan jihar, Ibrahim Bakori. Jami’an sun kama wani mutum mai suna Umar Danladi Usman mai shekaru 35 daga Kurna Layin Masallacin Juma’a, yayin da yake tuƙin wata mota ƙirar Honda Accord mai launin toka da gilashi masu duhu.
Kayayyakin da aka samu a hannunsa sun haɗa da bindigogi uku ƙirar AK-47 da aka ƙera, harsasai guda biyar, kwanson harsashin AK-47 guda ɗaya, da katin shaidar ɗan sanda na bogi, wuƙaƙe uku da kuma takalman jami’an tsaro irin na daji.
Rundunar ta ce yayin bincike wanda ake zargin ya amsa cewa ya samo bindigogin ne daga ƙaramar hukumar Dutsin-Ma ta jihar Katsina. ‘Yansanda sun ce ana ci gaba da bincike domin kamo sauran abokan hulɗarsa da kuma tarwatsa hanyar safarar makaman.
Kwamishinan ‘yansandan ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin tare da jaddada aniyar rundunar na yaƙi da safarar makamai, garkuwa da mutane da sauran manyan laifuka a jihar Kano. Ya kuma buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin ƙarfafa tsaro a jihar.















Discussion about this post