Manyan jam’iyyun adawa a ƙasar nan na shirin shiga sabon ƙawance da nufin gabatar da ƙalubale guda ɗaya ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Ƙawancen da ake shirin ƙullawa, wanda ƙungiyar G-100 ke jagoranta, na neman haɗa ADC, PDP, NDC, PRP, SDP da APM.
Ƴan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyun su ne: Atiku Abubakar (ADC), Peter Obi (NDC), Seyi Makinde (APM), Donald Duke (PRP), Adebayo Adewole Ebenezer (SDP) da Sanata Sandy Onor (PDP).
G-100, wadda tsohon Darakta-Janar na Progressiɓes Goɓernors’ Forum, Salihu Lukman, ke jagoranta, ya bayyana a wata sanarwa jiya cewa jam’iyyun adawa ba za su iya haɗa isasshen ƙarfin siyasa su kaɗai ba domin kayar da jam’iyyar da ke mulki. Saboda haka, ƙungiyar na matsa lamba a samar da ɗan takarar da kowa ya amince da shi da kuma dandalin siyasa guda ɗaya.
Shirin ya samu goyon baya daga wasu daga cikin jam’iyyun, sai dai masana harkokin siyasa sun ce burin kowane ɗan takara, hamayya tsakanin shugabannin adawa da kuma ƙarancin lokacin da ya rage kafin zaɓen 2027 na iya kawo cikas ga ƙoƙarin.
Ana sa ran G-100 za ta gudanar da taron ƙoli a ranar 18 ga Agusta, a wani ɓangare na ƙoƙarin samar da matsaya ɗaya tsakanin jam’iyyun adawa, ƴan takarar shugaban ƙasa, mataimakansu da shugabannin jam’iyyun na ƙasa.
Wannan sabon yunƙurin na farfaɗo da wani tsohon ƙoƙari ne da jam’iyyun adawa suka taɓa yi na samar da haɗin gwiwa. Irin wannan shawara ta taso a wani taron ƙoli da aka gudanar a Ibadan a watan Nuwamban bara, amma ta ƙasa haifar da ƙawance mai ɗorewa.
Yayin da wasu shugabannin adawa suka nuna shirinsu na bincikar wannan sabon tsarin, masana na ci gaba da nuna shakku kan ko ƴan takarar shugaban ƙasa da suka kwashe shekaru suna gina burinsu na siyasa za su amince su janye wa ɗan takarar da aka cimma matsaya a kansa.
Lokacin da aka tuntuɓi mafi yawan jam’iyyun da aka ambata a cikin wannan ƙoƙarin kafa ƙawance, sun tabbatar wa Daily Trust cewa suna sane da abin da ke faruwa kuma suna maraba da ra’ayin gudanar da taron, suna cewa wannan ita ce hanya mafi dacewa wajen tabbatar da sauyin da suke nema.
Lukman ya bayyana a wata hira da Trust TƁ cewa idan da gaske jam’iyyun adawa sun himmatu wajen ceto Nijeriya, abin farko shi ne su yi abin da ya dace domin bai wa ƴan Nijeriya tabbacin cewa akwai wata madadin gwamnati.
Ya ce: “Idan ba su haɗu wuri guda ba, ba na ganin ƴan Nijeriya za su damu da wannan batu. Kuma wannan shi ne saƙon da muka isar kuma har yanzu muke isarwa ga shugabannin jam’iyyun adawa.”
‘Atiku a shirye yake da duk wani tsari da zai hana Tinubu wa’adi na biyu’
Mai ba tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya ce ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC a shirye yake ya bi duk wani tsari da zai hana APC da Shugaba Tinubu samun wa’adi na biyu a mulki.
Ya shaida wa Daily Trust cewa, duk da cewa ba zai iya tabbatar da ko G-100 ta gana da Atiku ba, tsohon mataimakin shugaban ƙasar bai taɓa ja da baya daga ƙoƙarin kafa ƙawancen ba.
Ibe ya ce: “Shi (Atiku) yana cikin mutanen farko da suka fara tattaunawa kan yadda jiga-jigan adawa da ma jam’iyyun siyasa za su haɗu.
“Ya halarci taron da sanarwar Ibadan da aka gudanar a Jihar Oyo, duk da cewa wasu daga cikin waɗanda suka shiga wannan yunƙurin na Ibadan yanzu sun koma wasu jam’iyyun siyasa. Amma a wajensa, ban yi imanin cewa wani abu ya canza ba.
“Atiku Abubakar ya yi imanin cewa a zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya ya fi ƙarfi fiye da sanda ɗaya. Ina ganin Wazirin Adamawa ba zai guji duk wani abu da zai haɗa jam’iyyun adawa wuri guda ba.
“Abin da G-100 ke faɗa ya yi daidai da abin da shi ma yake faɗa tun shekarar da ta gabata bayan zaɓen ƙarshe. Ya fahimci a fili cewa wannan ita ce hanya mafi dacewa, kuma ƴan Nijeriya ma sun fahimci hakan, abin da ya haifar da wannan ƙawance.
“An samu sauye-sauye da dama tun daga lokacin, amma siyasa tana sauyawa a kodayaushe. Ina ganin zai kasance a shirye ya rungumi duk wani tsari da zai ba ƴan Nijeriya damar samun abin da suke so, tare da tabbatar da cewa APC da Shugaba Tinubu ba su samu wa’adi na biyu ba, domin ƴan Nijeriya su fara sake gina ƙasarsu.”
A nata ɓangaren, ADC ta ce a shirye take ta shiga kowace irin alaƙa ko haɗin gwiwa da wata jam’iyyar siyasa da ke da ra’ayi da manufofi masu kama da nata.
Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na ADC, Mallam Bolaji Abdullahi, ya kuma shaida wa ɗaya daga cikin wakilanmu cewa jam’iyyar ba ta adawa da ƙoƙarin kafa wannan ƙawance.














