ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Matashin Dan Siyasa ‘Al’ajabin Zazzau’

by Sani Anwar
3 weeks ago
Siyasa

Mahmud Sadis Buba mai shekaru 30 ya jawo hankula sosai tun bayan bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar mazabar tarayya ta Sabon Gari a Jihar Kaduna.

Matashin zai fafata neman tikitin jam’iyyar APC da dan majalisa mai ci, Sadik Ango Abdullahi, dan fitaccen dattijon kasa, Farfesa Ango Abdullahi.

Buba, wanda aka fi sani da lakabin “Al-ajabin Zazzau” saboda karfinsa da girmansa, ya ja hankalin jama’a a ciki da wajen mazabar, inda masu bibiyar siyasa da dama ke sa ido kan yadda tasirinsa ke karuwa.

ADVERTISEMENT

Mazabar tarayya ta Sabon Gari ana kallonta a matsayin daya daga cikin mazabu mafi tsananin gasa a siyasar Jihar Kaduna. Mazabar na da fitattun ‘yan siyasa da suka hada da Mataimakin Shugaban APC na shiyyar Arewa maso Yamma, Garba Datti Babawo; tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Aminu Abdullahi Shagali; da tsohon Shugaban PDP na Jihar Kaduna, Sa’in Jama’a.

Mazabar, wadda ta kunshi gundumomi 13, tana dauke da cibiyoyin gwamnatin tarayya da dama tare da al’umma mabambanta, abin da ke sanya fafatawa a zaben ke zama mai zafi.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Buba, wanda ke zaune tare da iyayensa a Layin Ambassador da ke Samaru a Zariya, bai yi aure ba kuma sabo ne a harkar neman mukamin zabe.

Yayin da wasu ‘yan siyasa da farko suka dauki aniyarsa a matsayin neman suna kawai, wasu yanzu suna kallonsa a matsayin babban dan takara saboda alakarsa da manyan ‘yan siyasa a matakin jiha da na kasa.

Wasu daga cikin magoya bayan dan majalisa mai ci, Sadik Ango Abdullahi, na kallon shigar Buba cikin takarar a matsayin wasan kwaikwayo kawai da kuma yunkurin neman suna a yankin.

Wani magoyin bayan APC a Samaru, Malam Ali “Go Slow,” ya bayyana Buba a matsayin matashin mai iya tara jama’a, wanda a baya ya rike mukamin shugaban kungiyar goyon bayan “Tinubu–Uba Sani Agenda 2027.”

Ya ce kuruciyar kamannin Buba ta haifar da ce-ce-ku-ce sosai a kafofin sada zumunta bayan hotuna da bidiyon tantancewarsa a Abuja sun bazu.

“‘Yan Nijeriya da dama sun yi mamakin yadda yake kama da karamin yaro duk da cewa yana neman kujerar Majalisar Tarayya. Wasu ma suna bayyana shi a matsayin daya daga cikin matasa mafi kankanta masu neman takara,” in ji shi.

Ali ya kara da cewa Buba ya gaji tasirin siyasa daga danginsu, domin mahaifinsa na da alaka da tsohon jakadan Nijeriya a Senegal, Amb. Sule Buba.

Bincike ya kuma nuna cewa dan takarar ya kulla alaka da manyan ‘yan siyasa a kasar nan, inda aka gan shi a hotuna tare da Shugaba Bola Tinubu, Gwamna Uba Sani, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio da sauran manyan shugabanni na kasa.

An ce ya fara jan hankalin jama’a ne jim kadan bayan zaben 2023 lokacin da hotunansa tare da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari suka bayyana a kafofin sada zumunta.

Wani mazaunin Samaru, Idris Umar, ya tunatar da cewa Buba ya raba buhunan shinkafa ga mazauna yankin a lokacin azumin Ramadan a matsayin wani bangare na ayyukan jin kai da yake yi.

“Duk da irin girmansa da karfinsa, mutane da dama a nan suna sonsa saboda ayyukan taimakon jama’a da yake yi. Amma kayar da dan majalisa mai ci ba zai kasance mai sauki ba domin yana da tushe sosai a siyasa,” in ji Umar.

Masu lura da al’amuran siyasa na ganin cewa dan majalisa mai ci, Sadik Ango Abdullahi, har yanzu yana da gagarumin goyon bayan jama’a, musamman ganin yadda ya lashe zaben fidda gwani na PDP yana cikin hannun masu garkuwa da mutane, sannan ya lashe babban zaben 2023 da rinjaye mai yawa.

Ana kuma ganin dan majalisar mai ci na cin gajiyar tasirin siyasar mahaifinsa, Farfesa Ango Abdullahi, wanda tsohon dan takarar gwamna ne a Jihar Kaduna, tsohon mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron abinci, kuma shugaban kungiyar dattawan Arewa ta Northern Elders Forum a yanzu.

Sai dai masu nazarin siyasa na cewa Buba na wakiltar sabon karni na matasa masu alakar siyasa da ke neman karin damar shiga shugabanci da gudanar da mulki.

Gabatar da takardun neman takararsa da ya yi ga Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Seyi Tinubu, da sauran manyan ‘yan siyasa ya kara jawo hasashe kan yadda tasirinsa ke karuwa a cikin APC.

Magoya bayansa na bayyana shi a matsayin matashi mai kuzari kuma mai kusanci da talakawa, yayin da wasu ke kallon fitowarsa a matsayin alamar karuwar shigar matasa cikin siyasar Nijeriya.

Sun ce idan Buba ya samu tikitin APC sannan ya lashe zaben, zai iya zama daya daga cikin mafi kankantar shekaru a Majalisar Dokoki ta 11 ta Nijeriya.

Martani dai na ci gaba da yawo a kafofin sada zumunta kan aniyarsa, inda mutane da dama ke bayyana shi a matsayin sabon fuska a siyasa.

Idan Buba ya kai ga shiga Majalisar Wakilai, ba zai zama mafi karancin shekaru a wannan zamani ba, domin Ibrahim Bello Mohammed, mai wakiltar mazabar tarayya ta Birnin Kebbi/Kalgo/Bunza a Jihar Kebbi, ya hau kujerar majalisa a shekarar 2023 yana da shekaru 27 kacal.

Siyasa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza
Labarai

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro
Manyan Labarai

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
Next Post
NJC Ya Dakatar Da Alƙalan Kotuna 2, Ta Ƙara Wa Wasu 12 Girma

NJC Ya Dakatar Da Alƙalan Kotuna 2, Ta Ƙara Wa Wasu 12 Girma

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.