Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, da Peter Obi da Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, sun bayyana cewa a shirye suke su amince da tsarin fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya domin ƙalubalantar APC a zaɓen 2027.
Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin haɗa kan manyan ‘yan adawa a ƙarƙashin wani sabon ƙawance da nufin haɗa karfi waje guda kafin babban zaɓen 2027.
Atiku, da Obi da Makinde sun nuna cewa muradinsu shi ne ganin an samu haɗin kai tsakanin ‘yan adawa, musamman domin rage rabuwar ƙuri’un masu adawa da gwamnatin APC.
Rahotanni sun nuna cewa batun wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa na haɗakar na daga cikin muhimman batutuwan da ake tattaunawa a kai, yayin da ake ƙoƙarin cimma matsaya da za ta samu karbuwa daga ɓangarori daban-daban.
Yunƙurin haɗakar na ƙara samun karɓuwa yayin da jam’iyyun siyasa ke fara shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027, inda ake sa ran batun fitar da ɗan takara guda zai kasance ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da ƙawancen zai fuskanta.














