Hukumar Rabar da Tattalin Arzikin Kasa, RMAFC ta bayyana cewa, ta na kan ci gaba da gudanar da aikin tantantace da kuma tattara sahihan bayanai, a daukacin fadin kasar bisa nufin tsara yadda za a rabar da tattalin azrkin kasa ga matakn gwamnati uku na kasar.
Kwamishina a hukumar a Farfesa Adekunle Wright, ya sanar da haka lokacin da ya jagoranci tawagar hukumar zuwa jahar Kebbi domin kaddamar da aikin. wanda ya gudana a birnin Kebbi, babban birnin jihar.
A jawabinsa a wajen kaddamawar mataimakin gwamnan jahar Abubakar Umar-Tafida, ya baiwa tawagar tabbacin goyon bayan gwamnatin jahar.
Wright ya danganta aikin a matsayin mai matukar mahimmanci wanda kuma zai taimaka wajen tattara sahihan bayanai da za su sanya a rabar da tattalin arzikin kasar ga matakan gwamnati uku na kasar, ba tare da, an tauyewa kowa hakkinsa ba.
Ya kara da cewa, sashe na 42 ‘ B’ a cikin Baka ba kundin tsarin mulkin kasar ne, ya dorawa hukumar nauyin gudanar da wannan aikin.
A cewarsa, sauyin da aka samu a bangaren tafiyar da tattalin arzikin kasa da karuwar alummar kasar da kuma karin wasu ci gaba da aka samu a kasar, ne suka sanya ya zama wajibi, a gudanar da wannan aikin.
Wright ya kuma yabawa gwamnatin jihar bisa tarbar girmamawa da suka yiwa tawagar hukumar,musamman irin tarbar ban girma da kwamishina kudi ta jihar Hajiya Rakiya Tanko-Ayuba, ta yiwa tawagar.
Ya ci gaba da cewa, a shekarar 2022, hukumar ta shirya wa wasu ma’aikatan jihar taron bita musamman domin su samu kwarewa, kan ilimin tattara sahihan bayanai na tara kudaden shiga, ga gwamnatin jihar..
Wright ya jaddada cewa, samun nasarar wannan aikin, ya dogara ne kachokam daga bangaren ma’aikatan gwamnati na jihar da kuma na kananan hukumomin jihar.
Ya yi nuni da cewa, sakamakon aikin zai amfani jihar da kuma kasa baki daya, inda kuma ya nanata kudurin hukumar wajen ganin, an gudanar da aikin bisa nuna kwarewa da kum yin gaskiya
Shi kuwa mataimakin gwamnan jihar Sanata Abubakar Umar-Tafida, ya bai wa hukumar tabbacin cewa, gwamnatin jihar a shirye take ta bayar da goyon bayan ta, domin a samu cin nasarar aikin.
Umar-Tafida ya kara da cewa, gwamnatin jihar a shirye take domin ta bayar da duk sahihan bayanai da hukumar ke bukata.
Ya yi nuni da cewa, sai idan an samar da sahihan bayanai ne, gwamnatin, za ta iya samun damar yin tsare-tsaren bunkasa jihar, musamman domin a kara bunkasa rayuwar alummar jihar baki daya















Discussion about this post