ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rabar Da Tattalin Arzikin Kasa: Hukumar RMAFC Ta Kaddamar Da Aikin Tattara Sahihan Bayanai

by Abubakar Abba
2 months ago
RMAFC

Hukumar Rabar da Tattalin Arzikin Kasa, RMAFC ta bayyana cewa, ta na kan ci gaba da gudanar da aikin tantantace da kuma tattara sahihan bayanai, a daukacin fadin kasar bisa nufin tsara yadda za a rabar da tattalin azrkin kasa ga matakn gwamnati uku na kasar.

Kwamishina a hukumar a  Farfesa Adekunle Wright, ya sanar da haka lokacin da ya jagoranci tawagar hukumar zuwa jahar Kebbi domin kaddamar da aikin. wanda ya gudana a birnin Kebbi, babban birnin jihar.

A jawabinsa a wajen kaddamawar mataimakin gwamnan jahar Abubakar Umar-Tafida, ya baiwa tawagar tabbacin goyon bayan gwamnatin jahar.

ADVERTISEMENT

Wright ya danganta aikin a matsayin mai matukar mahimmanci wanda kuma zai taimaka wajen tattara sahihan bayanai da za su sanya a rabar da tattalin arzikin kasar ga matakan gwamnati uku na kasar, ba tare da, an tauyewa kowa hakkinsa ba.

Ya kara da cewa, sashe na 42 ‘ B’ a cikin Baka ba kundin tsarin mulkin kasar ne, ya dorawa hukumar nauyin gudanar da wannan aikin.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

A cewarsa, sauyin da aka samu a bangaren tafiyar da tattalin arzikin kasa da karuwar alummar kasar da kuma karin wasu ci gaba da aka samu a kasar, ne suka sanya ya zama wajibi, a gudanar da wannan aikin.

Wright ya kuma yabawa gwamnatin jihar bisa tarbar girmamawa da suka yiwa tawagar hukumar,musamman irin tarbar ban girma da kwamishina kudi ta jihar Hajiya Rakiya Tanko-Ayuba, ta yiwa tawagar.

Ya ci gaba da cewa, a shekarar 2022, hukumar ta shirya wa wasu ma’aikatan jihar taron bita musamman domin su samu kwarewa, kan ilimin tattara sahihan bayanai na tara kudaden shiga, ga gwamnatin jihar..

Wright ya jaddada cewa, samun nasarar wannan aikin, ya dogara ne kachokam daga bangaren ma’aikatan gwamnati na jihar da kuma na kananan hukumomin jihar.

Ya yi nuni da cewa, sakamakon aikin zai amfani jihar da kuma kasa baki daya, inda kuma ya nanata kudurin hukumar wajen ganin, an gudanar da aikin bisa nuna kwarewa da kum yin gaskiya

Shi kuwa mataimakin gwamnan jihar Sanata  Abubakar Umar-Tafida, ya bai wa hukumar tabbacin cewa, gwamnatin jihar a shirye take ta bayar da goyon bayan ta, domin a samu cin nasarar aikin.

Umar-Tafida ya kara da cewa, gwamnatin jihar a shirye take domin ta bayar da duk sahihan bayanai da hukumar ke bukata.

Ya yi nuni da cewa, sai idan an samar da sahihan bayanai ne, gwamnatin, za ta iya samun damar yin tsare-tsaren bunkasa jihar, musamman domin a kara bunkasa rayuwar alummar jihar baki daya

RMAFC
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
RMAFC

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.