Gabanin zaben 2027, fatan samun hadin gwiwar ‘yan adawa don yakar jam’iyyar mai mulki ta APC, na fuskantar babbar matsala bayan da manyan shugabanni suka bar hadiakar saboda sabbanin kan tikitin shugaban kasa.
Rahotanni sun nuna cewa hadakar wanda aka kafa karkashin jam’iyyar ADC, mai nufin kalubalantar neman sake zaben Shugaba Bola Tinubu karo na biyu.
A watan Maris na shekara ta 2025, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu suka yi hadaka da shirin kifar da Shugaba Tinubu a shekarar 2027.
A ranar 3 ga Yuli, shugabannin jam’iyyun adawa, ciki har da Peter Obi da sauran manyan ‘yan siyasa daga jam’iyyun adawa da jam’iyya mai mulki, suka karbi ADC a matsayin jam’iyyar adawa don fafatawa a zaben 2027.
Tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami sun kasance cikin manyan ‘yan jam’iyyar hadaka tare da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso da masu goyon bayansa suka cikin wannan jam’iyya a ranar 20 ga Maris, 2026 bayan sun bar NNPP.
Sai dai kuma mambobin hadakar sun samu rarrabuwar kai kwanan nan bayan da rikice-rikicen shugabanci da suka dabaibaye jam’iyyar da kuma neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyya.
An ruwaito cewa tattaunawa domin tikitin takarar shugaban kasa kawai ta hadu da cikas tsakanin magoya bayan Atiku da Obi, tare da sauran ‘yan takara da ke fafatawa don samun tikitin takarar shugabancin kasa.
A ranar 2 ga Yuli, Ralph Nwosu, wanda ya kafa jam’iyyar kuma tsohon shugabanta, ya sanar da yin murabus na jagorantar kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, wanda ya bude hanya ga tsarin shugabanci na rikon kwarya da Dabid Mark ke jagoranta.
A wasu watanni bayan da Dabid Mark ya karbi jagorancin jam’iyyar, wani tsagin jam’iyyar da Nafiu Bala, daya daga cikin mataimakan shugaban jam’iyyar ke jagoranta ya kalubalanci tsarin.
Bala ya bayyana cewa bai taba yin murabus daga mukaminsa ba, ya yi ikirarin cewa shi ya kamata ya maye gurbin shugaban jam’iyyar bayan murabus din tsohon shugasaban jam’iyyar, kamar yadda aka bayyana a cikin kundin tsarin jam’iyyar.
Bala ya bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar ADC tare da shigar da kara a kotu kan kalubalantar shugabancin Mark. A ranar 2 ga Satumba, 2025, Bala ya nemi babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da shugabancin Mark.
Haka kuma ya nemi umarnin kotu don hana hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi amfani da sunan Mark a matsayin shugaban jam’iyyar tare da tilasta INEC ta saka sunansa a matsayin shugaban jam’iyyar na wucin gadi.
Har ila yau, ya shigar da bukatun kotu don dakatar da jam’iyyar yin duk wani taro har zuwa lokacin da za a yanke hukuncin kotu.
An fara sauraron shari’ar a ranar 4 ga Satumba, 2025, kuma alkalin kotun, Emeka Nwite, ya umarci a bai wadanda ake kara ciki har da INEC, sanar da su dalilin da ya sa ake karar.
Ba tare da gamsuwa da hukuncin wucin gadi ba, Dabid Mark ya shigar da koke yana kalubalantar hurumin babban kotun tarayya kan ci gaba da sauraron karar Bala.
Duk da haka, a ranar 12 ga Maris, 2026, kotun daukaka kara ta ki karbar karar Mark gaba daya, ta ce ba ta da hurumin zartar da hukunci ba tare da sanin tushen al’amari ba, wanda ya sa al’amarin ya tafi kotun koli.
Hukumar zabe, daga baya ta dakatar da bangaren Dabid Mark daga jagorancin jam’iyyar.
A ranar 30 ga Afrilu, kotun koli ta mayar da shugabancin Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC.
Duk da cewa kotun kolin ta soke umarnin kotun daukaka kara wanda ta umarci bangarorin su ci gaba da rike matsayinsu, ta tsaya ba tare da fitar da hukunci na karshe kan rikicin shugabanci da ke kasa ba.
A cikin hukuncin kotun koli mai alkalai biyar karkashin jagorancin Alkali Mohammed Lawal Garba, ta yanke hukunci cewa kotun daukaka kara ta yi aiki fiye da karfin ikonta ta hanyar bayar da umarni bayan ta ki amincewa da karar da aka shigar a gabanta.
Kotun ta amince kawai da wani bangare na daukakar karar Mark kuma ta umarci dukkan bangarorin su koma kotun daukaka kara don ci gaba da sauraron karar.
Masana sun ci gaba da cewa daya daga cikin manyan dalilan rarrabuwar shugabannin ‘yan adawa shi ne, rashin ikon jam’iyyar na tsara shugabancinta bisa yankuna.
Yayin da Atiku da magoya bayansa ke shirin samun tikitin shugaban kasa na ADC daga shugabannin jam’iyya, Obi yana ganin cewa shi ya fi cancanta, yana tabbatar da cewa har yanzu yankin kudanci ya kamata ya fitar da shugaban kasa.
Bangaren Obi ya zargi Atiku da shirin bai wa shugabannin jam’iyya kudi don ba shi damar samun tikiti.
Sakamakon lamarin ya haifar da rashin jituwa, wanda ya sa Obi da Kwankwaso a ranar Lahadi suka dauki matakin komawa jam’iyyar NDC suka bar ADC.















Discussion about this post