ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 months ago
ADC

Gabanin zaben 2027, fatan samun hadin gwiwar ‘yan adawa don yakar jam’iyyar mai mulki ta APC, na fuskantar babbar matsala bayan da manyan shugabanni suka bar hadiakar saboda sabbanin kan tikitin shugaban kasa.

Rahotanni sun nuna cewa hadakar wanda aka kafa karkashin jam’iyyar ADC, mai nufin kalubalantar neman sake zaben Shugaba Bola Tinubu karo na biyu.

A watan Maris na shekara ta 2025, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu suka yi hadaka da shirin kifar da Shugaba Tinubu a shekarar 2027.

ADVERTISEMENT

A ranar 3 ga Yuli, shugabannin jam’iyyun adawa, ciki har da Peter Obi da sauran manyan ‘yan siyasa daga jam’iyyun adawa da jam’iyya mai mulki, suka karbi ADC a matsayin jam’iyyar adawa don fafatawa a zaben 2027.

Tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami sun kasance cikin manyan ‘yan jam’iyyar hadaka tare da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso da masu goyon bayansa suka cikin wannan jam’iyya a ranar 20 ga Maris, 2026 bayan sun bar NNPP.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sai dai kuma mambobin hadakar sun samu rarrabuwar kai kwanan nan bayan da rikice-rikicen shugabanci da suka dabaibaye jam’iyyar da kuma neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyya.

An ruwaito cewa tattaunawa domin tikitin takarar shugaban kasa kawai ta hadu da cikas tsakanin magoya bayan Atiku da Obi, tare da sauran ‘yan takara da ke fafatawa don samun tikitin takarar shugabancin kasa.

A ranar 2 ga Yuli, Ralph Nwosu, wanda ya kafa jam’iyyar kuma tsohon shugabanta, ya sanar da yin murabus na jagorantar kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, wanda ya bude hanya ga tsarin shugabanci na rikon kwarya da Dabid Mark ke jagoranta.

A wasu watanni bayan da Dabid Mark ya karbi jagorancin jam’iyyar, wani tsagin jam’iyyar da Nafiu Bala, daya daga cikin mataimakan shugaban jam’iyyar ke jagoranta ya kalubalanci tsarin.

Bala ya bayyana cewa bai taba yin murabus daga mukaminsa ba, ya yi ikirarin cewa shi ya kamata ya maye gurbin shugaban jam’iyyar bayan murabus din tsohon shugasaban jam’iyyar, kamar yadda aka bayyana a cikin kundin tsarin jam’iyyar.

Bala ya bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar ADC tare da shigar da kara a kotu kan kalubalantar shugabancin Mark. A ranar 2 ga Satumba, 2025, Bala ya nemi babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da shugabancin Mark.

Haka kuma ya nemi umarnin kotu don hana hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi amfani da sunan Mark a matsayin shugaban jam’iyyar tare da tilasta INEC ta saka sunansa a matsayin shugaban jam’iyyar na wucin gadi.

Har ila yau, ya shigar da bukatun kotu don dakatar da jam’iyyar yin duk wani taro har zuwa lokacin da za a yanke hukuncin kotu.

An fara sauraron shari’ar a ranar 4 ga Satumba, 2025, kuma alkalin kotun, Emeka Nwite, ya umarci a bai wadanda ake kara ciki har da INEC, sanar da su dalilin da ya sa ake karar.

Ba tare da gamsuwa da hukuncin wucin gadi ba, Dabid Mark ya shigar da koke yana kalubalantar hurumin babban kotun tarayya kan ci gaba da sauraron karar Bala.

Duk da haka, a ranar 12 ga Maris, 2026, kotun daukaka kara ta ki karbar karar Mark gaba daya, ta ce ba ta da hurumin zartar da hukunci ba tare da sanin tushen al’amari ba, wanda ya sa al’amarin ya tafi kotun koli.

Hukumar zabe, daga baya ta dakatar da bangaren Dabid Mark daga jagorancin jam’iyyar.

A ranar 30 ga Afrilu, kotun koli ta mayar da shugabancin Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC.

Duk da cewa kotun kolin ta soke umarnin kotun daukaka kara wanda ta umarci bangarorin su ci gaba da rike matsayinsu, ta tsaya ba tare da fitar da hukunci na karshe kan rikicin shugabanci da ke kasa ba.

A cikin hukuncin kotun koli mai alkalai biyar karkashin jagorancin Alkali Mohammed Lawal Garba, ta yanke hukunci cewa kotun daukaka kara ta yi aiki fiye da karfin ikonta ta hanyar bayar da umarni bayan ta ki amincewa da karar da aka shigar a gabanta.

Kotun ta amince kawai da wani bangare na daukakar karar Mark kuma ta umarci dukkan bangarorin su koma kotun daukaka kara don ci gaba da sauraron karar.

Masana sun ci gaba da cewa daya daga cikin manyan dalilan rarrabuwar shugabannin ‘yan adawa shi ne, rashin ikon jam’iyyar na tsara shugabancinta bisa yankuna.

Yayin da Atiku da magoya bayansa ke shirin samun tikitin shugaban kasa na ADC daga shugabannin jam’iyya, Obi yana ganin cewa shi ya fi cancanta, yana tabbatar da cewa har yanzu yankin kudanci ya kamata ya fitar da shugaban kasa.

Bangaren Obi ya zargi Atiku da shirin bai wa shugabannin jam’iyya kudi don ba shi damar samun tikiti.

Sakamakon lamarin ya haifar da rashin jituwa, wanda ya sa Obi da Kwankwaso a ranar Lahadi suka dauki matakin komawa jam’iyyar NDC suka bar ADC.

ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?
ADC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 32 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Katsina

Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 32 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.