ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
4 weeks ago
ADC

Gabanin zaben 2027, fatan samun hadin gwiwar ‘yan adawa don yakar jam’iyyar mai mulki ta APC, na fuskantar babbar matsala bayan da manyan shugabanni suka bar hadiakar saboda sabbanin kan tikitin shugaban kasa.

Rahotanni sun nuna cewa hadakar wanda aka kafa karkashin jam’iyyar ADC, mai nufin kalubalantar neman sake zaben Shugaba Bola Tinubu karo na biyu.

A watan Maris na shekara ta 2025, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi da tsohon shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu suka yi hadaka da shirin kifar da Shugaba Tinubu a shekarar 2027.

ADVERTISEMENT

A ranar 3 ga Yuli, shugabannin jam’iyyun adawa, ciki har da Peter Obi da sauran manyan ‘yan siyasa daga jam’iyyun adawa da jam’iyya mai mulki, suka karbi ADC a matsayin jam’iyyar adawa don fafatawa a zaben 2027.

Tsohon ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami sun kasance cikin manyan ‘yan jam’iyyar hadaka tare da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso da masu goyon bayansa suka cikin wannan jam’iyya a ranar 20 ga Maris, 2026 bayan sun bar NNPP.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Sai dai kuma mambobin hadakar sun samu rarrabuwar kai kwanan nan bayan da rikice-rikicen shugabanci da suka dabaibaye jam’iyyar da kuma neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyya.

An ruwaito cewa tattaunawa domin tikitin takarar shugaban kasa kawai ta hadu da cikas tsakanin magoya bayan Atiku da Obi, tare da sauran ‘yan takara da ke fafatawa don samun tikitin takarar shugabancin kasa.

A ranar 2 ga Yuli, Ralph Nwosu, wanda ya kafa jam’iyyar kuma tsohon shugabanta, ya sanar da yin murabus na jagorantar kwamitin gudanarwa na jam’iyyar, wanda ya bude hanya ga tsarin shugabanci na rikon kwarya da Dabid Mark ke jagoranta.

A wasu watanni bayan da Dabid Mark ya karbi jagorancin jam’iyyar, wani tsagin jam’iyyar da Nafiu Bala, daya daga cikin mataimakan shugaban jam’iyyar ke jagoranta ya kalubalanci tsarin.

Bala ya bayyana cewa bai taba yin murabus daga mukaminsa ba, ya yi ikirarin cewa shi ya kamata ya maye gurbin shugaban jam’iyyar bayan murabus din tsohon shugasaban jam’iyyar, kamar yadda aka bayyana a cikin kundin tsarin jam’iyyar.

Bala ya bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar ADC tare da shigar da kara a kotu kan kalubalantar shugabancin Mark. A ranar 2 ga Satumba, 2025, Bala ya nemi babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da shugabancin Mark.

Haka kuma ya nemi umarnin kotu don hana hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi amfani da sunan Mark a matsayin shugaban jam’iyyar tare da tilasta INEC ta saka sunansa a matsayin shugaban jam’iyyar na wucin gadi.

Har ila yau, ya shigar da bukatun kotu don dakatar da jam’iyyar yin duk wani taro har zuwa lokacin da za a yanke hukuncin kotu.

An fara sauraron shari’ar a ranar 4 ga Satumba, 2025, kuma alkalin kotun, Emeka Nwite, ya umarci a bai wadanda ake kara ciki har da INEC, sanar da su dalilin da ya sa ake karar.

Ba tare da gamsuwa da hukuncin wucin gadi ba, Dabid Mark ya shigar da koke yana kalubalantar hurumin babban kotun tarayya kan ci gaba da sauraron karar Bala.

Duk da haka, a ranar 12 ga Maris, 2026, kotun daukaka kara ta ki karbar karar Mark gaba daya, ta ce ba ta da hurumin zartar da hukunci ba tare da sanin tushen al’amari ba, wanda ya sa al’amarin ya tafi kotun koli.

Hukumar zabe, daga baya ta dakatar da bangaren Dabid Mark daga jagorancin jam’iyyar.

A ranar 30 ga Afrilu, kotun koli ta mayar da shugabancin Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC.

Duk da cewa kotun kolin ta soke umarnin kotun daukaka kara wanda ta umarci bangarorin su ci gaba da rike matsayinsu, ta tsaya ba tare da fitar da hukunci na karshe kan rikicin shugabanci da ke kasa ba.

A cikin hukuncin kotun koli mai alkalai biyar karkashin jagorancin Alkali Mohammed Lawal Garba, ta yanke hukunci cewa kotun daukaka kara ta yi aiki fiye da karfin ikonta ta hanyar bayar da umarni bayan ta ki amincewa da karar da aka shigar a gabanta.

Kotun ta amince kawai da wani bangare na daukakar karar Mark kuma ta umarci dukkan bangarorin su koma kotun daukaka kara don ci gaba da sauraron karar.

Masana sun ci gaba da cewa daya daga cikin manyan dalilan rarrabuwar shugabannin ‘yan adawa shi ne, rashin ikon jam’iyyar na tsara shugabancinta bisa yankuna.

Yayin da Atiku da magoya bayansa ke shirin samun tikitin shugaban kasa na ADC daga shugabannin jam’iyya, Obi yana ganin cewa shi ya fi cancanta, yana tabbatar da cewa har yanzu yankin kudanci ya kamata ya fitar da shugaban kasa.

Bangaren Obi ya zargi Atiku da shirin bai wa shugabannin jam’iyya kudi don ba shi damar samun tikiti.

Sakamakon lamarin ya haifar da rashin jituwa, wanda ya sa Obi da Kwankwaso a ranar Lahadi suka dauki matakin komawa jam’iyyar NDC suka bar ADC.

ADC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
ADC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Yanzu-yanzu: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Zuwa NDC
Tambarin Dimokuradiyya

Kwararan Sauye-sauyen Da Obi Da Kwankwaso Suka Jawo A Siyasar Nijeriya Gabanin Cikar Wa’adin INEC

May 9, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 32 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Katsina

Sojoji Sun Kuɓutar Da Mutane 32 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Katsina

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.