Dakarun rundunar haɗin gwuiwa ta Operation FANSAR YAMMA tare da jami’an Katsina State Community Watch Corps sun samu nasarar kuɓutar da mutane 32 da aka yi garkuwa da su tare da kashe ‘yan ta’adda biyu a wani sumame da suka kai a jihar Katsina.
An gudanar da aikin ceton ne da sanyin safiyar Juma’a, 8 ga watan Mayu, 2026, a ƙauyen Dikawa da ke ƙaramar hukumar Matazu, bayan samun sahihan bayanan sirri kan motsin ‘yan ta’addan da suka ɓoye mutanen da suka sace a yankin.
A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar, ya ce dakarun sun yi artabu mai zafi da ‘yan bindigar bayan isa maboyarsu, lamarin da ya tilasta musu tserewa tare da barin waɗanda suka sace.
Sanarwar ta ce an kashe ‘yan ta’adda biyu yayin fafatawar, sannan an kuɓutar da mutum 32 da suka haɗa da maza 9, mata 10 da yara 13. Dakarun sun kuma lalata sansanonin da maboyar ‘yan ta’addan domin hana su sake amfani da yankin wajen aikata laifuka.
An kuma ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu, da sinƙin harsasai masu yawa, da wani gurneti na hannu da aka ƙera a gida, da babura 10 da kuma dabbobi 26 da aka sace. Rundunar ta ce an kai waɗanda aka ceto wuraren tsaro domin kula da lafiyarsu tare da yaba wa al’umma bisa ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai.















Discussion about this post