ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
Atiku

Lokacin da tsohon Sanata Dino Melaye ya wallafa a shafukan sada zumunta cewa Peter Obi zai iya aiki ne kawai a karan kansa, nan take ya zama daya daga cikin batutuwan siyasa mafi shahara a makon nan.

Kusan makonni biyu kacal bayan da shugabannin ‘yan adawa sun taru a Ibadan suka yi alkawarin yin hadaka kafin zaben 2027, hadakan ‘yan adawan Nijeriya tuni ya fada cikin rikici.

“Peter Obi ya tusa kansa cikin yanayi mai wuya. Zai iya aiki ne kawai a karan kansa, wanda hakan kuma ya saba wa ka’idar siyasar da muke ciki a yanzu,” Melaye ya rubuta.

ADVERTISEMENT

Rahotonni sun bayyana cewa kwanakin bayan Obi da Rabiu Musa Kwankwaso suka bar jam’iyyar ADC, zuwa NDC, wanda hakan ya jefa sabon rashin tabbas cikin kokarin gina hadaka na manyan jam’iyyun adawa domin yakar APC.

Ga yawancin ‘yan Nijeriya, abubuwan da suka faru sun tuna musu zaben shugaban kasa na 2023, lokacin da rabuwar kawunan ‘yan adawa ta taimaka wajen bude kofar nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu duk da fushin mutane game da wahalhalun tattalin arziki da rashin tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

Tsoron da yawancin magoya bayan ‘yan adawa ke yi na cewa tarihi na iya maimaita kansa.

A lokacin zaben 2023, Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa da kuri’u kimanin miliyan 8.79, kusan kashi 37 cikin dari na jimillar kuri’un da aka jefa.

Yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya samu kuri’u kusan miliyan 6.98, yayin da Obi ya samu kusan miliyan 6.10. Kwankwaso ya samu kuri’u miliyan 1.5, mafi yawansu daga Kano da wasu sassan yankunan arewa maso yamma. Idan aka hada su, manyan ‘yan takarar adawa sun sami kuri’u fiye da na Tinubu.

Amma tsarin zaben Nijeriya ya ba dan takarar da ke da karfi tsosai wani gwarin gwiwa fiye a kasa da samun hadin kai a fadin yankuna da ke kasar nan. APC kuma ta amfana daga karancin masu jefa kuri’a da kuma rarrabuwar kawunan ‘yan adawa.

Wannan sakamakon ya haifar da rashin jin dadi a tsakanin magoya bayan ‘yan adawa, da dama daga cikinsu har yanzu suna da yakinin cewa hadakar ‘yan adawa zai iya canza sakamakon.

Taron ‘yan adawa na Ibadan da aka gudanar a ranar 25 ga Afrilu, 2026, an yi shi ne don magance wannan matsalar.

‘Yan siyasa daga kungiyoyi daban-daban na hamayya sun hallara don nuna hadin kai da tattauna yiwuwar cimma yarjejeniya kafin zaben 2027.

Haka kuma taron ya samar da wani babban alkawari na yin aiki tare wajen yin adawa da APC da kuma jure abin da masu jawabi suka bayyana a matsayin kokarin mai da Nijeriya tsarin jam’iyya guda.

A wani bangaren kuma, taron ya haifar da kwarin gwiwar cewa ‘yan adawar Nijeriya sun dauki darasi daga kurakuran da suka tabka a shekarar 2023.

A ranar 3 ga Mayu, hadin gwiwar ‘yan adawa ya shiga cikin matsala bayan Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso suka shiga jam’iyyar NDC a hukumance, wanda ya zama sun fice daga ADC, wanda ya rushe tattaunawar Ibadan. Wannan lamari ya sauya lissafin ‘yan adawa kafin shekarar 2027.

Maimakon samun hadin gwiwar adawa guda daya mai karfi, yanayin siyasa yanzu yana bayyana cewa an samu rarrabuwar kawuna, bangaren Atiku na ci gaba da kasancewa a cikin jam’iyyar ADC, Obi da Kwankwaso sun hada kai a cikin jam’iyyar NDC, sauran ‘yan siyasa har yanzu suna nazarin yiwuwar hadin kai.

Fadar shugaban kasa za ta yi amfani da rikicin ‘yan adawa don samun nasara.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya zargi Obi da kauce wa fafatawar siyasa masu wuya da kuma canza jam’iyya a duk lokacin da zai fuskanci zaben fitar da gwani.

Rahotanni sun nuna cewa rarrabuwar ‘yan adawa zai iya sake bai wa Tinubu daman sake lashe zabe a 2027.

Lissafin APC yana da sauki, rarrabuwar kawunan ‘yan adawa na rage yiwuwar kalubale mai zafi da zai iya barazanar ga jam’iyyar mai mulki.

A halin yanzu, jam’iyyun adawa suna ta kokarin gamsar da ‘yan Nijeriya cewa sun samar musu ta wata zabi da zai yaki APC kai tsaye.

Mafi yawancin ‘yan Nijeriya da ke fuskantar kunci na tattalin arziki, harkikin siyasa da ake yi a kai a kai yana kara jin kamar ba ya da alaka da abubuwan da ake fuskanta a rayuwar yau da kullum. Don haka, fushin jama’a ba a kan jam’iyyar mai mulki kawai ba ne, amma yana karuwa ga masu fafutukar samun iko ko ta halin kaka.

A yanzu haka, rabewar ‘yan adawa za ta taimaka wa Tinubu. A kowanne mako ana gudanar da sauya sheku, rikice-rikicen cikin gida, da hare-haren jama’a lokaci ne da ake amfani da shi wajen gina kamfen din siyasa.

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Yanzu-yanzu: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Zuwa NDC
Tambarin Dimokuradiyya

Kwararan Sauye-sauyen Da Obi Da Kwankwaso Suka Jawo A Siyasar Nijeriya Gabanin Cikar Wa’adin INEC

May 9, 2026
Next Post
Atiku

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Karfafa Bincike A Fannin Kiwon Dabbobi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.