Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi ta Tarayya, ta sanar da cewa; ta fara gudanar da aikin binciken fannin a daukacin fadin kasar.
A cewarta, manufar aikin shi ne, domin kara karfafa tattara bayanai da tsara tsarin fannin da kuma zuba jari a fannin na kiwon dabbobin.
Binciken, zai karade gurare har guda 67 da ake sa ran za a tattara sahihan bayanai da za a mika wa gwamnatin tarayya, domin duba irin kokarin da ake yi na bunkasa fannin a daukacin fadin wannan kasa.
A cewar ma’aikatar, ana sa ran gudanar da aikin bisa gaskiya da bin ka’ida.
Idan za a iya tunawa, daga tsakanin ranar 20 zuwa ranar 24 na watan Afirilun 2026, aka fara gudanar da aikin wanda ya mayar da hankali, wajen gudanar da tattaunawa da masu ruwa da tsaki da ke fannin.
Har ila yau, ma’aikatar ta kara da cewa; aikin ya mayar da hankali ne a bangaren kiwon shanu da samar da madarar shanu da kiwon kajin gidan gona da na tumakai da awakai da sauransu.
A cewar ma’aikatar, za a yi amfani da sakamakon binciken, domin auna irin nasarorin da aka samu a daukacin fadin wannan kasa.
Ta kara da cewa, ana sa ran za a fitar da sakamakon binciken, nan da mako mai zuwa, wanda hakan zai kara taimakawa kan kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi na samar da wadataccen abinci a fadin kasar da kara habaka tattalin arzikin kasar tare da kuma inganta rayuwar ‘yan kasar baki-daya.















Discussion about this post