ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A.A. Zaura Ya Wakilci Gwamna Abba Wajen Karɓo Lambar Yabo A Legas

by Muhammad Bashir
7 months ago
Zaura

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya samu lambar yabo ta Gwamnan Shekara 2025 daga jaridar The Sun, bisa la’akari da irin nasarorin da ya samu a fannin shugabanci da gudanar da mulki.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanyawa hannu a ranar Lahadi.

  • 2023: Matsin Lamba Ba Za Ta Sa Na Janye Takarata Ba – A.A Zaura
  • Yanzu-yanzu: Mahaifiyar A.A. Zaura Ta Shaki Iskar ‘Yanci

An miƙa lambar yabon ne a wani biki da aka gudanar a Eko Hotels, Jihar Legas, inda Sanata Orji Uzor Kalu ya gabatar da kyautar, tare da halartar manyan jami’an gwamnati da fitattun mutane daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

An karɓi lambar yabon a madadin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta hannun Alhaji Abdulkareem A. Zaura (A.A. Zaura). A wajen bikin, an kuma karrama wasu gwamnonin jihohin Zamfara da Cross River.

Haka kuma, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya samu lambar yabo ta Sanatan Jin-ƙai na Shekara.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Da yake jawabi bayan karɓar lambar yabon, A.A. Zaura ya bayyana cewa wannan karramawa wata babbar ƙarfafa guiwa ce ga Gwamna Abba Kabir Yusuf domin ƙara ƙaimi wajen samar da ingantaccen mulki ga al’ummar Jihar Kano. Ya ce wannan yabo bai zo da mamaki ba, duba da yadda gwamnan ya kasance ɗaya daga cikin gwamnonin da aka fi yaba wa a ‘yan kwanakin nan, sakamakon manufofinsa na jin daɗin al’umma da ayyukan da ake gani a fili.

Ya tunatar da cewa a shekarar 2025 kaɗai, Gwamna Yusuf ya samu lambobin yabo guda biyar da suka shafi ilimi, ciki har da ta Gwamnan da Ke Kaunar Malamai daga Ƙungiyar Malaman Nijeriya (NUT), da kuma yabo daga jaridun LEADERSHIP, Blueprint da New Telegraph.

A cewarsa, an kuma karrama gwamnan da lambobin Gwamnan Da Ke Son Ma’aikata da Gwamnan Da Ke Son Tsofaffin Ma’aikata, bayan biyan sama da Naira biliyan 27 na bashin fansho da garatuti.

Zaura

Zaura ya ƙara da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kafa tarihi a matsayin gwamna na farko da ya aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 71,000, wanda ke nuna jajircewar gwamnatinsa wajen kare walwalar ma’aikata.

Cikin tawagar da ta halarci bikin akwai tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Malam Muhammad Garba da tsohon Shugaban Ma’aikatan Jiha, Usman Bala da Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Yaɗa Labarai, Ibrahim Adam da Darakta Janar, Asma’u Jibril da kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sadaukar da wannan lambar yabo ga al’ummar Jihar Kano, bisa ga goyon baya, haɗin kai da addu’o’in da suke masa. Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da ƙarin ribar dimokiraɗiyya tare da hanzarta bunƙasar jihar baki ɗaya.

Zaura
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
Next Post
2027: Atiku Ya Yi Ganawar Sirri Da Shugabannin Jam’iyyar ADP Kan Jita-Jitar Takarar Obi Da Kwankwaso

2027: Atiku Ya Yi Ganawar Sirri Da Shugabannin Jam’iyyar ADP Kan Jita-Jitar Takarar Obi Da Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Zaura

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Zaura

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.