Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana farin cikinsa yayin da aka fara jigilar maniyyata Hajjin bana kai tsaye daga ciki sauka da tashin jirage na Gusau International Airport zuwa Saudiyya.
Jirgin farko ya tashi ne a jiya Juma’a ɗauke da maniyyata 415 na jihar Zamfara a cikin jirgin Max Air mai lamba NGL270. Daga cikin maniyyatan akwai maza 288 da mata 127.
Da yake jawabi yayin ƙaddamar da jirgin, Dauda Lawal ya bayyana aikin gina filin jirgin a matsayin babban aikin tarihi na gwamnatinsa. Ya ce mutane da dama sun yi shakku kan yiwuwar kammala aikin, amma yau an tabbatar da hakan bayan fara aikin ginin a ranar 18 ga Yunin 2024.
Gwamnan ya ce maniyyatan jihar yanzu za su samu damar tafiya cikin sauƙi kai tsaye daga Gusau zuwa Saudiyya cikin ƙasa da awa huɗu, sabanin baya da suke zuwa Kano ko Sakkwato kafin su samu jirgin Hajji.
Ya kuma bayyana cewa gwamnati ta fara tattaunawa da kamfanonin jiragen sama domin fara zirga-zirgar jiragen kasuwanci daga filin jirgin na Gusau, yana mai roƙon maniyyatan su yi addu’a ga jihar Zamfara da kuma Nijeriya yayin gudanar da ibadar Hajji.















Discussion about this post