Hada-hadar kasuwanci, a karkashin shugabancin Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwan na Kasa Dakta Abubakar Dantsoho, na ci gaba da tumbatsa, a Tashoshin da ke a jihar Legas.
Wannan na zuwa ne, yayin da Jiragen Ruwa guda 16_ dauke da kayan da suka hada da, Man Fetur da Danyen Mai da kayan abinci, suka sauka a Tashoshin biyu da ke a jihar Legas.
A cikin sanarwar da hukumar ta NPA ta fitar a jihar ta bayyana cewa. Jiragen Ruwan guda 16, sun sauka ne a Tashoshin Apapa, Tin Can Island da ta Lekki .
Hukumar ta sanar da cewa, Jiragen sun iso ne, dauke da Man Fetur da Danyen mai da Iskar Gas da takin Urea da sauran kayan abinci.
Ta kara da cewa, ana kuma ci gaba da jiran wasu Jiragen Ruwa guda 34, da za su sauka a Tashoshin Jiragen Ruwan na jihar Legas daga ranar 6 zuwa ranar 18 na watan Mayun 2026 wadanda za su yi dakon kaya, kamar su Buhunhunan Alkama da Danyen Kifi da Man Dizil da Danyen Mai da Buhunhunan Waken Soya da sauransu.
Rahotanni sun bayyana cewa, a yanzu haka, akwai Jiragen Ruwa guda 23 da ke kan sauke kayan da suka yo jigilar su a Tashoshin Jiragen Ruwan da ke a jihar Legas.
Kayan da suke kan sauke wa, sun hada da, Man Jirgin samada Man Fetur da tsakin Urea da Alkama da Danyen Kifi da sauransu.















Discussion about this post