ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Magance Karancin Abinci Mai Gina Jiki A Nijeriya

by Leadership Hausa
3 months ago
Abinci

A bisa kokarin da ake yi magance kalubalen rashin abinci mai gina jiki musamman a tsakanin yara kanana da kuma kara karafawa iyalai a daukacin fadin kasar nan guwai, hakan ya sanya, a kwnan baya, Sanata Remi Tinubu, mai dakin shugaban kasa,ta kaddamar da wani shiri na kasa, domin a magance wannan matsalar.

A jawabinta a yayin kaddamarwar Remi da alakanta wannan matsalar a matsayin gagarumar matsala wadda ake bukatar a magance ta, matakin kasa, a karkashin wannan shirin.

Shirin dai, za a  fara wanzar da shi ne gadan-gadan a cikin watan Afirilun wannan shekarar, wanda kuma aka tsara shi musamman domin inganta samar da abinci mai gina jiki a tsakanin marasa karfi da yara da shekarun su, suka faa daga shekaru shida.

ADVERTISEMENT

A cewar Remi, za a gudanar da shirin ne a hukumomin kiwon kula da kiwon lafiya na farko da ke a daukacin fadin kasar, inda a  nan ne, za gudanar da yin rijistar iyalan da aka zabo domin amfana da shirin.

Ta kara da cewa, wadanda za su amfana, za a wayar masu da kai da kuma raba masu kayan abinici masu gina jiki da aka noma a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Taron kadamawar, ya samu halartar Sarakunan Gargajiya, Malaman Addini Ministan kiwon lafiya Farfesa Muhammad Pate ya sanar da cewa, kimanin yara kanana kaso 40 a cikin dari a kasar, na fuskantar matsalar karamcin abinci mai gina jiki, wanda ya ce, wannann matsalar, na fara ne, tun kafin a haifi yaran.

A cewarsa, rashin abinci mai gina jiki, na kara haddasa mutuwar yara kanana, tun suna gakiyar tasowarsu, da hana su samun ingantaccen ilimi da fuskantar kalubale na dogon zango a rayuwarsu.

A bisa ra’ayin mu a  wannan Jaridar yakar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara kanana a kasar abu ne, da yake da matukar mahimanci, musamman duba da cewa, a duk makon farko na kowanne watan Agustan shekara, ana gudanar da fadakarwa ta duniya kan mahimmancin shawar da jarirai  Nonon Uwa.

Kazalika, tun kafin a fara fustantar kalubalen rashin tsaro a kasar, da kuma dimbin abincin da ake da shi a kasar, yara kanana na ci gaba da fuskantar karancin abinci mai gina jiki.

A wasu shekarun baya, Asusun Tallafawa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya wato  UNICEF ta yi hadaka da shirin samar da abinci wato RUTF na Gwamnatin Tarayya wa, musamman wannan shirin an samar da shi ne, yadda za a rinka yin amfani Gydar da aka sarrafa, domin magance babbar matsalar karancin abinci mai gina jiki a Arewacin Nijeriya.

Bugu da kari, shayar da Jarirai Nonon Uwa zalla, ya ci gaba da kasance kan akalla kaso 29 a cikin dari, a wan Agustan 2025, inda hakan ya nuna shayarwar, ta ragu da kaso 50 a cikin dari, kamar yadda Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Duniya da Gwamnatin Tarayya, suka ayyana ana son a cimma

A cewar UNICEF, duk da cewa, mata masu shayarwa a kasar, sun kirkiro da tsarin shayarwa da ya kao kaso 90 a cikin dari, amma har yanzu, ana ci gaba da kai wa wata shida na sahayar da Jarirai Nonon Uwa, wanda hakan ya nuna cewa, akwai bukatar kara samar da tsare-tsare da bayar da goyon baya, a guraren yin aiki yadda mata ma’aikata masu shayarwa, za su samu karin damar shayar  da Jariransu, a wajen da suke yin aiki.

A shekaru da dama da suka gabata Gwamnatin Tarayya ta sha kikiro da dauki iri da ban da ban na magance kalubalen rashin abinci mai gina jiki, a tsakanin yara kanana, sai dai, Gwamnatin na samar da daukin ne kawai, na wucin gadi.

Bugu da kari, wannan Jaridar za ta iya tunawa, a shekarar 2025, Gwmantin Tarayya ta kiriro da wani shiri na samar da abinci mai gina jiki wanda aka kaddamar, a kananan hukumomi 774 da ake da su a kasar.

Bayan wannan kaddamarwar, babban taro na kasa na samar sa abinci mai gina jiki da kuma samar da wadataccen abinci, ya biyo baya.

Taron, ya samu halartar kwararru daga fannoni da ban da ban, ministoci, hukumomin gwamnati, hukumomin tsaro, Sarakunan Gargajiya, ‘yan majalisar taraya da majalisun dokkki da sauran abokan hadaka.

Mataimakin Shugaban Kasa Sanata Kashim Shettima, wanda ya kaddamar da bude taron ya bukaci, da samar da dabarun kara inganta samar da abinci mai gina jiki da kuma wadataccen abinci a kasar.

Sai dai, batun, ba wai kawai halartar Sarakunan Gargajiya da Mlaman Addainai waje kaddamarwa bane, akwai kuma matukar bukatar, su kara zage damtse wajen fadadar da alumomin su, kan mauhimmancin ciyar da yara kanana abinci, mai gina jiki, duba da cewa, ana samun koma baya, wajen ciyar da yaran, wadanda sune, manyan gobe.

Wannan Jaridar na yin la’akari da cewa, ko da yake kundin tsarin mulkin kasar na 1999 da aka sabunta, bai bai wa Sarakunan damar bayar da wata gudunmawa ba, amma suna taimaka wa, wajen wanzar da zaman lafiya da warware rikice-rikice.

Daga watan Afirilun 2025, bisa wasu rahoton da Bankin Duniya ya fitar, sun nuna cewa, akalla ‘yan Nijeriya kaso 75.5, na ci gaba da zaman cikin talauci.

Bugu da kar, yawan masu zama a cikin talauci a karkara, sun rubanya yawan mazauna a birne,  inda a karkara, ake da kaso 41.3.

Bisa bincken kiwon lafiya da aka gudanar daga 2023 zuwa 2024  na NDHS da kuma fashin bakin da aka yi a kwanan baya kan karancin abnci mai gina jiki, daga 2024 zuwa 2025, hakan ya nuna cewa, yara kanana ‘yan shekaru kasa da biyar da ke fama da karancin abinci maras jina jiki,  da ke zaune a karkara, sun kai sama da kaso 50.

Akwai kuma bukatar Sarakunan Gargajiya, su rinka fadadar musamman mata, kan mahimmancin shayar da Jarirai, Nonon Uwa.

Sai dai, abin damuwar mu shi ne, hujjoji da dama a baya sun nuna cewa, irin wannan daukin da ake samarwa, a karshe, ana yin watsi da shi ne, ba tare da wadanda ake da burin su amfana ba, sun ci gajiyar daukin ba.

A kasar nan, ba wai an gaza samar da tsare-tsare bane, amma matsalar itace, rashin wanzar da tsare-tsaren, yadda ya kamata.

A kwanan baya, an ruwaito shugaba Bola Tinubu ya sanar da cewa, ana samar da ingantacciyar kiwon lafiya, hakan ne zai sanya, a samar da yara manyan gobe, wajen gina kasa.

A lokacin yana raye, tsohon shugaban kasar Amurka John F. Kennedy, ya bayyana cewa, yara sune babban ginshikin yari, a duk fadin duniya kuma wadanda ake da babban fana, samar masu da gobe, mai kyau.

Abinci
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Yakin Iran: Duniya Na Fuskantar Tsadar Kayan Abinci Da Man Fetur

Yakin Iran: Duniya Na Fuskantar Tsadar Kayan Abinci Da Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.