ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet

by Darlington Uzodinma and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
5 days ago

Akwai ƙaruwar damuwa game da tusshen hanyoyin samun kuɗaɗen ƴan ta’adda da sauran ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba. Hasalima damuwar ta zama babban batun da ya shafi ƙasa a yayin da ya bayyana ƙarara cewa wasu marasa kishin ƙasa da kuma masu aikata ɓarna na ba da gudummawa ga ayyukan ta’addanci ta hanyar zama hanyar samar da kuɗaɗen da ake amfani da su wajen aiwatar da miyagun laifuka a bisa ga wata manufar siyasa da ta da zaune tsaye.

Babban abin da ya ƙara ɗaukar hankalin jama’a shi ne yadda tsarin hada-hadar kuɗi na duniya ya ɗauki lamarin da muhimmanci, kuma Nijeriya ba za ta zauna abaya ba, musamman ganin yadda ƙasar ke ƙara zama ɗaya daga cikin cibiyoyin ayyukan ta’addanci.

Ko shakka babu ta’addanci da nau’o’insa kama daga kan fashi da makami da garkuwa da mutane sun sun zama ruwan dare a ƙasar nan a yau suna kuma haifar da tsananin damuwa ga jama’a da iyalansu.

ADVERTISEMENT

Ba sai mutum ya fuskanci irin wannan lamari kai tsaye ba sa’annan zai fahimci irin ƙunchi da illar da hakan ke haifarwa, haka ma ba tare da la’akari da asarar kuɗi ba waɗanda ko da an biya kuɗin fansa babu tabbacin wanda aka sace zai koma gida da ran sa.

A yayin da wannan matsalar ta kai ƙololuwa, an fara zargin cibiyoyin hada-hadar kuɗi wato bankuna da masu harkokin  canjin kuɗi a matsayin waɗanda ake zargin suna taka rawa a lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

A bisa ga tsananin wannan matsalar, musamman yadda take da matuƙar illa ga tsaron ƙasa, ya sanya hukumomin kula da harkokin kudlɗi da na tattalin arziki cikin matsin lamba domin ɗaukar matakan yaƙi da samar da kuɗaɗen ta’addanci tare da tabbatar da ɗaukar matakan inganta tsaron yanar gizo.

A kan wannan Babban Bankin Ƙasa ya tashi tsaye wajen tunkarar wannan ƙalubale ta hanyar aiwatar da sababbin manufofi da matakai domin tabbatar da tsarin aikinsu da hanyoyin gudanar da harkokinsu ba su gurɓace ba ko fadawa hannun ayyukan da ke barazana ga muradun tsaron ƙasa ba.

Domin cimma wannan buri na tabbatar da ganin ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba, ba su yi anfani da tsarin banki da harkokin kuɗi ba, babban bankin ƙasar ya ƙara tsaurara sa ido kan bankunan ajiya da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗi.

Haka kuma Babban Bankin ya gudanar da binciken ba- zata a kan bankunan Nijeriya da rassansu na ƙasashen waje domin hanzarta cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da ake sanyawa ido a yadda suke tafiyar da harkokin kuɗaɗe.

Babban Bankin Nijeriya ya ɗauki wannan mataki ne domin samar da ingantaccen yanayin zuba jari, jawo hankalin masu zuba jari daga ƙasashen waje da kuma ƙarfafa martabar tsarin kuɗi na Nijeriya a idon duniya.

Bugu da ƙari, bankin ya ci- gaba da dagewa wajen ƙarfafa tsaron yanar gizo ta hanyar kafa ingantaccen tsarin sa ido a dukkanin ɓangarorin hada-hadar kuɗi a inda ya umurci bankuna da sauran cibiyoyin da yake kula da su da su gudanar da cikakken nazarin kan su domin auna ƙarfin su na jure hare-haren yanar gizo.

Wannan mataki ya tabbatar da cewa bankunan ajiya, bankunan sabis na biyan kuɗi, ƙananan cibiyoyin ba da rance , kamfanonin turawa da karɓar kuɗi da sauran cibiyoyin hada-hadar kuɗi sun bi wannan doka a inda a cikin ƙanƙanin lokaci suka kammala amfani da sabon tsarin da aka ƙaddamar na kayan aikin tantance ƙarfin tsaron yanar gizo.

Wannan ya haɗa da tsari mai inganci da aka tsara domin tantance yadda cibiyoyin ke fuskantar barazanar hare-haren yanar gizo da kuma ƙarfin su na ɗaukar matakan kariya tare da mayar da martani.

Babban ginshiƙin tsarin waɗannan manufofin shi ne ƙoƙarin samar da ƙwaƙƙwaran sa- ido bisa la’akari da haɗurra daga ɓangaren hukumomin sa- ido.

Babbar manufar wannan tsari ita ce samar da saurin bunƙasar bankin zamani da biyan kuɗi ta hanyar na’ura domin ƙara amincewar masu amfani da ayyukan tare da rage guraben da masu aikata laifukan yanar gizo za su iya kai hari da kuma taƙaita sauran ɓangarori masu rauni a tsarin da ke iya haddasa matsaloli.

Wannan umarni ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara nuna damuwa kan barazanar hare-haren yanar gizo da ke kai hari ga cibiyoyin hada-hadar kuɗi a faɗin duniya, yayin da ƙaruwar dogaro da harkokin kuɗaɗe na zamani, masu samar da ayyuka na waje da kuma tsarin ajiya na gajimare ke ƙara fallasa bankuna ga haɗurra masu rikitarwa da ke ci- gaba da sauyawa.

Ga ɓangaren bankunan Nijeriya, a na sa ran wannan manufa za ta ƙara tsaurara buƙatun bin ƙa’idoji tare da hanzarta zuba jari a fannin kayan aikin tsaron yanar gizo, tsarin shugabanci da kuma hanyoyin kaucewa haɗurra.

Ƙananan cibiyoyi, ciki har da ƙananan bankuna da kamfanonin turawa da karɓar kuɗi na iya fuskantar ƙarin tsadar daidaitawa yayin da suke ƙokarin bin sabbin sharuɗɗan da aka gindaya.

Kamar yadda Babban Bankin Ƙasa ya bayyana, wannan ƙoƙarin hadin guiwar zai tattara cikakkun bayanai kan tsarin shugabanci na tsaron yanar gizo, hanyoyin kiyaye haɗurra, yadda ake mu’amala da masu ba da sabis na waje, ƙarfin mayar da martani ga hare-hare da kuma jimillar ƙarfin jure matsaloli na tsarin aiki baki ɗaya.

A na sa ran sakamakon da za a samu daga wannan aikin zai jagoranci matakan sa- ido na hukumomi tare da ƙarfafa kulawa da dokoki kan haɗurran fasahar zamani a faɗin ɓangaren hada-hadar kuɗi baki ɗaya.

A yayin da babban bankin ƙasa ya ƙaddamar da wannan yunƙuri na yaƙi da haramtacciyar hanyar samar da kuɗaɗen ta’addanci ta hanyar ƙarfafa amincewa da tsarin tsaron yanar gizo, ya dogara kan haɗin kai da gaskiyar cibiyoyin da ke ƙarkashin ikon sa inda bankin ya bayyana matsayinsa a fili cewa za a ɗauki mataki kan duk wani rahoto da aka gano ba daidai ba a ƙoƙarin ɓoye gaskiya.

Masana sun bayyana cewa matakin da Babban Bankin Ƙasa ya ɗauka na iya ƙara ƙarfafa amincewa da tsarin hada- hadar kuɗi ta hanyar tabbatar da cewa cibiyoyin kuɗi sun rungumi matakan kariya masu inganci da tsauri domin daƙile aukuwar hare-haren yanar gizo da ka iya kawo cikas ga ayyuka ko rage amincewar kwastomomi.

Amfani da tsarin gamsuwar abokan ciniki, ya sanya Nijeriya a layi ɗaya da sabbin matakan da duniya ke bi, inda manyan bankuna ke kara mayar da hankali kan ƙarfafa tsaro a tsarin harkokin kuɗi domin tabbatar da kwanciyar hankali a fannin hada-hadar kuɗi, musamman yayin da harkokin kuɗi na zamani ke ƙara faɗaɗa a ƙasashe masu tasowa

A kan wannan a bayyane yake Babban Bankin Ƙasa bai yi ƙasa a guiwa ba domin ya ƙara ƙaimi wajen aiwatar da matakan yaƙi da safarar kuɗaɗen haram da kuma tabbatar da tsaron yanar gizo.

Haka kuma Babban Bankin ya ƙara tsaurara sa- ido tare da gudanar da binciken ba- zata a kan bankunan Nijeriya da rassansu a ƙasashen waje domin hanzarta fitar da Nijeriya daga jerin ƙasashen da aka sa wa idanu. Waɗannan matakai na da manufar samar da ingantaccen yanayin zuba jari, jawo masu zuba jari daga ƙasashen waje, da kuma ƙara ɗaukaka martabar tsarin kuɗi na Nijeriya a idon duniya.

Darlington Uzodinma
+ posts Bio
    This author does not have any more posts.
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ posts Bio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Yadda Rashin Aikin Yi Ke Jefa Matasa Maula Da Bangar Siyasa

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22

Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.