ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Magidanci

A duk yayin da mace ta dauki ciki, tana samun kanta a wani irin yanayi maras dadi har sai ta haihu, don haka; batun juna biyu ba karamin al’amari ba ne, sakamakon zuwa da ya ke yi da hadari iri daban-daban.

Wasu matan, bayan sun dauki ciki ne suke haduwa da cututtuka da dama; kamar ciwon zuciya, ciwon siga, hawan jini da sauran makamantansu. Don haka, a nan ya kamata a sani cewa; babu yadda za a yi mace ta dauki ciki ba tare da jikinta ya canza ba.

  • Shettima Ya Ce Zuba Jari A Ɓangaren  Ilimi Ba Caca Ba Ce
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Dangane Da Dalilan Dadaddiyar Al’adar Ziyarar Da Ministocin Harkokin Wajen Sin Ke Fara Yi A Afirka A Duk Shekara

Wannan dalili ne ya sa, idan nauyin mai juna biyu bai kai yadda ake bukata ba, sai a ja hankalinta ta yi wasu abubuwa da za su sa nauyin nata ya karu, haka nan; idan nauyin nata ya yi yawa, musamman ga mata masu kiba; nan ma a kan ja hankalinsu su yi kokari wajen rage nauyin nasu.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, da zarar an ce mace na da ciki; abubuwa da dama na sauya yanayin jikinta, wata ta kara kiba, wata kuraje su feso mata a fuska, wata kalar fatarta ta canja; wani wajen ya yi fari wani ya yi baki, wasu su yi ta samun kananan cututtuka, wasu amai, wasu kuma saboda damuwa su yi ta faman kuka ba tare da an yi musu komai ba.

Don haka, ya zama wajibi maza su rika yi wa matansu uzuri a yayin da suke dauke da juna biyu da kuma bayan sun haihu. Misali, babu yadda za a yi a ce mace ta dauki ciki tsawon wata tara tana tare da shi, sannan bayan ta haihu a kuma yi tunanin cewa; wannan ciki nata zai dawo kamar yadda yake a baya.

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Har ila yau, maza da dama na da irin wannan dabi’a ta tsangwamar matansu, sakamakon yadda jikinsu yake sauyawa bayan sun haihu, musamman ganin yadda cikinsu yake yin shaida ko tattarewa ko kuma girma ta hanyar samun tumbi.

Irin wannan tsangwamar da maza ke yi wa mata, ko kadan bai dace ba; domin kuwa wasu matan na shiga cikin mummunan hali tare da takurawa kansu, ta hanyar kashe kudadensu don ganin sun samu maganin wannan matsala, wadda babu yadda za a yi a iya magance ta, tunda halittar ce a haka; kamar shekaru ne duk yadda za ka yi, babu wata dabara da za ta iya boye su.

Saboda haka, mata ya kamata ku kiyaye; ku daina zuwa kuna kashe kudadenku babu gaira babu dalili, amma babu wani magani da za a baki ki sha tumbinki ya tafi, wasu sai su sha magani su je su yi ta zawo haka kawai, wai don tunbinsu ya ragu.

A nan, muna kara jan hankalin maza; su ji tsoron Allah su rika tausaya wa matayensu, musamman bayan sun samu juna biyu sun haihu. Sannan ku tuna cewa, wannan ciki da yake canja wa mata wasu bangarori na jikinsu, ku ne kuke yi musu ba daga gidajensu suke zuwa da shi ba.

Daga rumbun Dakta Na’ima Abubakar

Magidanci
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Magidanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Next Post
aure

Yadda Ake Zama Da Uwar Miji

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.