ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Tauraruwarsu Ke Haskawa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
AFCON 2023

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Kamar yadda aka tsara, tuni aka fara gasar cin kofin Afirka a ranar 13 ga watan Janairu aka fara gasar cin kofin Afirka karo na 34, kuma za a kammala ranar 11 ga watan Fabrairu a kasar Ibory Coast, wadda ita ce mai masaukin baki.

Sai dai gasar ta wannan karon za ta samu bakuncin zakakuran ‘yan wasa da tauraruwarsu take haskawa a duniya kuma sun buga wasanni a gasar a shekarun baya kuma har yanzu suna haskawa.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • Kasar Sin Ta Harba Kumbon Dakon Kaya Domin Aikewa Da Kayayyaki Ga Tashar Sararin Samaniya

Fitattun ‘yan wasan nahiyar Afrika da suka yi fice a duniya sun fara baje-koli, tun daga ranar 13 ga watan Janairu zuwa 11 ga watan Fabrairu, LEADERSHIP HAUSA ta zakulo ‘yan wasan da tauraruwarsu ta fara haskawa.

Sadio Mané (Senegal)

Mane shi ne dan wasan da ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon Afirka na 2022 kuma dan wasan na tawagar Senegal zai sake fitowa idon duniya a wannan gasar, wadda kasarsa za ta yi yunkurin kare kambunta da zimmar komawa da shi gida.

Duk da yake, ya bar nahiyar Turai zuwa kasar Saudiyya da kwallo, Sadio Mane bai rasa kwarewarsa da zafin namansa ba ko kadan sannan shi ne hasken tawagar Senegal, kuma ba shi da burin da ya wuce lashe gasar karo na biyu a jere.

Bincent Aboubakar (Cameroon)

Yawanci a wasannin gasa mai yawa shi ne yake goya tawagar Kamaru a kafadarsa domin Bincent Aboubakar shi ne kyaftin din Kamaru kuma wanda ya fi ci musu kwallo a ‘yan shekarun bayan nan.

Kwarin gwiwarsa da kyakkywan fatan da ya ke da shi da kuma kwarewarsa a jagoranci su ne za su kan Kamaru ga nasarar lashe gasar karo na shida a tarihi kamar yadda suke fata.

Sébastien Haller (Côte d’Iboire, 30)

Karo na biyu kenan da zai buga gasar Afcon, ba shi da wani buri da ya wuce buga wannan gasa a gida gaban magoya bayan da suka karbe shi hannu biyu-biyu.

Sébastien Haller mai shekara 30 ya kai wata matuka da ake tsammanin zai nuna kansa a wannan gasa kamar yadda yake yi a nahiyar Turai.

Mohamed Amoura (Algeria)

A lokacin da manyan ‘yan wasan suka mamaye tawagar Algeria irinsu Mahrez Feghouli Slimani da sauransu, sabbin matasa irinsu Mohamed Amoura za su so a gabatar da su a matsayin sabbin fuskar gasar shekara ta 2023. Kuma hankali zai koma kansu muddin aka basu dama suka yi amfani da ita.

Matashin dan wasan tsakiyan, ya nuna kansa a kungiyarsa ta Belgium na tsawon kusan shekaru biyu, kuma ya taimaka wa kasarsa wajen kai wa ga manyan gasanni a ‘yan shekarun nan.

Bictor Osimhen (Nigeria)

Tawagar Super Eagles ta Nigeriya ta dade ba ta yi shahararren mai zura kwallo a raga ba kamar dan wasa Bictor Isimhen tun bayan marigayi Rasheed Yakini, kuma abu ne mai wahala ka fitar da wannan jerin sunaye babu gwarzon nahiyar Afrika na 2023.

Bictor Osimhen da ya zama gwarzo na bayan nan, ya sake samun daukaka a wasannin kwallo a nahiyarmu ta Afirka kuma shi ne yake jan ragamar tawagar Nijeriya, kuma hankali ya karkata kansa a Cote d’Iboire domin ganin rawar da zai taka.

André Onana (Cameroon)

A halin yanzu ga masu Kallon kwallon kafa a duniya, sunan mai tsaron ragar Kamaru da yake jan ragamar jaridu a nahiyar Turai kusan ko wane mako, saboda abin da yake kokari ko akasin haka a kungiyarsa ta Manchester United. Sai dai an fuskanci tazgaro da turjiya bayan da Manchester United ta bukaci mai tsaron ragar ya zauna ya buga wa kungiyar wasan da suka tashi 2-2 da kungiyar Tottenham a filin wasa na Old Trafford.

AFCON 2023
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.