ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Tauraruwarsu Ke Haskawa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
AFCON 2023

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Kamar yadda aka tsara, tuni aka fara gasar cin kofin Afirka a ranar 13 ga watan Janairu aka fara gasar cin kofin Afirka karo na 34, kuma za a kammala ranar 11 ga watan Fabrairu a kasar Ibory Coast, wadda ita ce mai masaukin baki.

Sai dai gasar ta wannan karon za ta samu bakuncin zakakuran ‘yan wasa da tauraruwarsu take haskawa a duniya kuma sun buga wasanni a gasar a shekarun baya kuma har yanzu suna haskawa.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • Kasar Sin Ta Harba Kumbon Dakon Kaya Domin Aikewa Da Kayayyaki Ga Tashar Sararin Samaniya

Fitattun ‘yan wasan nahiyar Afrika da suka yi fice a duniya sun fara baje-koli, tun daga ranar 13 ga watan Janairu zuwa 11 ga watan Fabrairu, LEADERSHIP HAUSA ta zakulo ‘yan wasan da tauraruwarsu ta fara haskawa.

Sadio Mané (Senegal)

Mane shi ne dan wasan da ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon Afirka na 2022 kuma dan wasan na tawagar Senegal zai sake fitowa idon duniya a wannan gasar, wadda kasarsa za ta yi yunkurin kare kambunta da zimmar komawa da shi gida.

Duk da yake, ya bar nahiyar Turai zuwa kasar Saudiyya da kwallo, Sadio Mane bai rasa kwarewarsa da zafin namansa ba ko kadan sannan shi ne hasken tawagar Senegal, kuma ba shi da burin da ya wuce lashe gasar karo na biyu a jere.

Bincent Aboubakar (Cameroon)

Yawanci a wasannin gasa mai yawa shi ne yake goya tawagar Kamaru a kafadarsa domin Bincent Aboubakar shi ne kyaftin din Kamaru kuma wanda ya fi ci musu kwallo a ‘yan shekarun bayan nan.

Kwarin gwiwarsa da kyakkywan fatan da ya ke da shi da kuma kwarewarsa a jagoranci su ne za su kan Kamaru ga nasarar lashe gasar karo na shida a tarihi kamar yadda suke fata.

Sébastien Haller (Côte d’Iboire, 30)

Karo na biyu kenan da zai buga gasar Afcon, ba shi da wani buri da ya wuce buga wannan gasa a gida gaban magoya bayan da suka karbe shi hannu biyu-biyu.

Sébastien Haller mai shekara 30 ya kai wata matuka da ake tsammanin zai nuna kansa a wannan gasa kamar yadda yake yi a nahiyar Turai.

Mohamed Amoura (Algeria)

A lokacin da manyan ‘yan wasan suka mamaye tawagar Algeria irinsu Mahrez Feghouli Slimani da sauransu, sabbin matasa irinsu Mohamed Amoura za su so a gabatar da su a matsayin sabbin fuskar gasar shekara ta 2023. Kuma hankali zai koma kansu muddin aka basu dama suka yi amfani da ita.

Matashin dan wasan tsakiyan, ya nuna kansa a kungiyarsa ta Belgium na tsawon kusan shekaru biyu, kuma ya taimaka wa kasarsa wajen kai wa ga manyan gasanni a ‘yan shekarun nan.

Bictor Osimhen (Nigeria)

Tawagar Super Eagles ta Nigeriya ta dade ba ta yi shahararren mai zura kwallo a raga ba kamar dan wasa Bictor Isimhen tun bayan marigayi Rasheed Yakini, kuma abu ne mai wahala ka fitar da wannan jerin sunaye babu gwarzon nahiyar Afrika na 2023.

Bictor Osimhen da ya zama gwarzo na bayan nan, ya sake samun daukaka a wasannin kwallo a nahiyarmu ta Afirka kuma shi ne yake jan ragamar tawagar Nijeriya, kuma hankali ya karkata kansa a Cote d’Iboire domin ganin rawar da zai taka.

André Onana (Cameroon)

A halin yanzu ga masu Kallon kwallon kafa a duniya, sunan mai tsaron ragar Kamaru da yake jan ragamar jaridu a nahiyar Turai kusan ko wane mako, saboda abin da yake kokari ko akasin haka a kungiyarsa ta Manchester United. Sai dai an fuskanci tazgaro da turjiya bayan da Manchester United ta bukaci mai tsaron ragar ya zauna ya buga wa kungiyar wasan da suka tashi 2-2 da kungiyar Tottenham a filin wasa na Old Trafford.

AFCON 2023
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.