ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

by Bello Hamza
4 months ago
Ruwan

Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta bayyana cewa, aikin zamanantar da Tashoshin Jiragen Ruwan kasar da a yanzu, ake ci gaba da yi da kuma wanzar da tsarin NSW, zai taimaka matuka, wajen rage asarar da kasar ke tabkawa, a duk shekara, wadda ta kai ta kimanin Naira tiriliyan daya, musamman saboda rashin da ake da shi, na kayan aiki na zamani.

Kazalika, Hukumar ta sanar da cewa, idan wannan tsarin na NSW ya fara aiki  gadan-gadan, a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, zai kara habaka kara samar wa da kasar kudaden shiga, a duk shekara, da suka kai daga kaso 10 zuwa 20, wadanda za su kai ga samun Naira biliyan 600 zuwa Naira tirliyan 1.2.

  • Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Sauya Fasalin Tsarin Tsaro A Yaki Da Ta’addanci
  • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin

Sama da samun karin kudaden shiga, tsarin ana kuma sa ran zai kara bunkasa hada-hadar kasuwanci da kuma rage jinjirin da ake samu na safarar kaya daga kaso 35 zuwa kaso 45 a cikin dari tare da kuma rage tsadar hada-hadar da kai ta kaso 25.

ADVERTISEMENT

Da yake yin tsokaci kan sauye-sauyen da aka samar a Hukuamr ta NPA, shugabanta na kasa Dakta Abubakar Dantsoho, ya bayyana cewa, magance gibin da ake da shi, a bangaren fasahar zamani, a fannnin na sufurin Jiragen Ruwa na kasar, abu ne da ya kasance, banbban ginshiki, na sauye-sauyen da da ake da shi, musamman a karkashin ajandar gwamnatin  shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Dantsoho ya kara da cewa, shirin ya zamanantar da Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan zai kara habaka hada-hadar kasuwanci a Tashoshin kasar da kuma yadda ake sauke kayan da aka yo jigilarsu, zuwa tashoshin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

A cewarsa, gwamnatin tarayya, ce ta kirkiro da aikin sabunta Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, musamman wajen bukatar samar da kayan aiki na zamani, a Tashoshin da ke a Apapa, Tin Can Island, Port Harcourt, Warri da kuma ta Calabar.

“Babbar manufar shi ne, domin a samar da kayan aiki na zamani da Tashoshin da kuma kara fadada yadda za a rinka sauke kayan a Tashoshin, masu yawan gaske tare da kara bunkasa hada-hadar kasuwanci, a Tashoshin,”.

Dantsoho ya kara da cewa, aikin zamanantar da Tashoshin, zai taimaka, wajen rage bata lokacin safarar kaya da rage tsadar hada-hadar tare da kuma samar da saukin yin kasuwanci, inda hakan za kara tabbatar da yin gasar kasuwanci, a fadin duniya.

Shugaban ya bayyana cewa, alamu sun nuna cewa, tuni, aka fara samun ci gaba a fannin na sufurin Jiragen Ruwan kasar, musamman wajen shigo da kaya a zuwa cikin Tashoshin wadanda suka karu daga kaso tan miliyan 45.1 zuwa kaso tan miliyan 103.3, inda kuma saukar Jiragen Ruwa a Tashoshin, ya karu zuwa sama da  4,000.

Kazalika, kwantainar da ake saukewa a Tashoshin, sun karu zuwa miliyan 1.74 wanda hakan ya nuna a zahiri, an samu karin hauhawan hada-hadar kasuwanci da kuma yawan Jiragen Ruwan da ke fitar da kaya, daga Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

Bugu da kari, Dantsoho ya sanar da cewa, yin amfani da kayan aiki wadanda ba na zamani ba, na rage yawan yadda ake gudanar da hada-hada, a Tashoshin, wanda hakan kuma, ke kara haifar da cunkoso, a Tashoshin da kuma kara bata lokacin jigilar Jiragen Ruwan.

Sai dai, shugaban ya bayyana cewa, aikin na zamanantar da Tashishin, zai taimaka, wajen fadada gudanar ayyuka a Tashoshin da kuma rage bata lokaci.

Dantsoho ya kara da cewa, kara ingnata kayan aiki da kuma kara habaka gudanar da ayyuka a Tashoshin, hakan zai rage tsada da kuma kara janyo hankali masu zuba jari daga kasashen waje.

Ya ci gaba da cewa, aikin zamantar da Tashohin, zai kuma taima samar da gudanar da hada-hada, a tsakanin kasashen da ke makwataka da kasar nan kamar irin su,jamhuriyar Benin, Togo da kuma Ghana.

Shugaban na hukumar ta NPA, ya kuma jaddada mahimmancin daga darajar Tashoshin, wanda ya sanar da cewa, hakan zai kara sanya gudanar da gasa a fannin na shurin Jiragen Ruwan kasar, musamman saboda sauye-sauyen na zamani, da hukumar ta samar.

A cewarsa, tsarin na NSW an tsara shi ta hanyar yin amfani da kafar zamani, musamman domin a bayar da dama, ga ‘yan kasuwa, yadda za su rinka gabatar da takardunsu na son yin fitar da kaya zuwa waje, ta hanyar gabatar da bukatarsu, a cikin rumbun samun bayanai ba tare da wani bata lokacin jiran hukumomin gwamnatin tarayya ba.

Dantsoho ya kara da cewa, tsarin na zamani na NSW zai kawar duk wani bata lokaci wajen yin hada-hadar kasuwanci da kuma tabbatar da ana bin ka’ida, wajen gudanar da ayyuka yadda suka kamata, a Tashoshin Jiragen Ruwan.

Bugu da kari, shugaban ya sanar da cewa, tsarin na zamani zai dakile duk wani kutse na bil’adama da magance almundahar cin hanci da rashawa da kuma dode duk wata kafa, da kudaden shiga na  gwamnti, ke zurarewa.

Shugaban hukumar ya kuma sanar da cewa,  hakan zai kuma  bayar da damar samun bayanai, a tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin wanda hakan zai kara taimaka wa, wajen daukar matakai, a hukumance.

Hakazalika,  sauye-sauyen, za su kara taimaka wa, wajen kara habaka kudaden shiga ga gwamnati da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Dantsoho ya kara da cewa, aikin zamantar da Tashoshin, zai taimaka wajen janyo hankalin masu zuba hannun jari a fannnin tattalin aarzikin kasar, kai tsaye.

Ya sanar da cewa, alfanun da tsarin na NSW da kuma aikin zamanantar da Tashoshin ke da shi, ya dara maganar kara bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

Ruwan
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Ministan Tsaron Nijeriya Ya Taya Al’ummar Musulmai Murnar Sallah

Ministan Tsaron Nijeriya Ya Taya Al'ummar Musulmai Murnar Sallah

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.