Fitacciyar ‘yar gwagwarmaya nan kuma ‘yar siyasa, Aisha Yesufu, ta sha kaye a zaɓen fidda gwani na kujerar Sanatan Babban Birnin Tarayya (FCT) na jam’iyyar NDC.
Ta sha kaye ne a hannun Amanda Pam, a zaɓen da aka gudanar gabanin babban zaɓen 2027.
Aisha Yesufu ta ce tana neman kujerar ne domin kawo sauyi a Abuja da kuma bai wa mazauna birnin ƙwarin gwiwa a harkokin gwamnati.
An kuma san ta da kasancewa babbar mai goyon bayan ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC, Peter Obi.
Bayan sakamakon, wasu masu amfani da kafafen sada zumunta sun yi martani, inda wasu suka ce siyasa tana buƙatar ƙarfi da tsari, ba kawai shahara a kafafen sada zumunta ba.
Sakamakon ya nuna cewa Amanda Pam ce za ta wakilci jam’iyyar a takarar Sanatan Abuja a zaɓen 2027.















Discussion about this post