Paris Saint-Germain na neman lashe kofin Gasar Zakarun Turai karo na biyu a jere yayin da za ta kara da Arsenal a wasan ƙarshe da za a buga a Budapest.
A bara, PSG ta lashe kofin karo na farko bayan doke Inter Milan da ci 5 da babu, wanda ya zama mafi girman tazarar da aka taɓa samu a wasan ƙarshe na gasar.
Mai horar da ƙungiyar, Luis Enrique, ya sauya fasalin ƙungiyar bayan ficewar fitattun ‘yan wasanta kamar Lionel Messi, Neymar da Kylian Mbappe.
‘Yan wasa irin su Ousmane Dembele da Khvicha Kvaratskhelia sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin PSG a bana.
PSG na fatan zama ƙungiyar farko tun bayan Real Madrid da za ta lashe Gasar Zakarun Turai sau biyu a jere.














Discussion about this post