ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

by Abdullahi Muh'd Sheka and Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kanawa

Tun bayan karbar rantsuwar Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin zababben gwamna Jihar Kano ya fara aiwatar da abubuwan da ya alkawarta wa Kanawa, musamman kan gine-ginen da gwamnatin jihar karkashin Abdullahi Umar Ganduje ta gina.

Domin nuna wa Kanawa da gaske gwamnatin NNPP take tun bayan rantsar da shi, gwamnan ya fara dirar mikiya a filin sukuwa da ke unguwar masu hannu da shuni ta Nasarawa, inda Gwamna Abba ya kaddamar da rushe wasu rukunin kantuna guda 90 da ake zargin na dan Gwamna Ganduje ne.

  • Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana 12 Ga Watan Yuni, Ranar Hutu

Daga nan ne kuma ya dira a tsohon otal din Daula, wanda Gwamnatin Abba ta zargi Ganduje da yin watandar filin, sai kuma tsohon gidan Jaridar Triump wanda aka tsara mayar da shi wurin kasuwar masu canjin kudaden kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Ita ma kasuwar masaukin alhazai ta gamu da sabon matakin gwamnatin, inda nan ma aka tabbatar da tarwatsa wuraren da aka rabar wa wasu masu kwalli a ido kamar yadda sabuwar gwamnatin ta ce.

Cikin daren Lahadin da ta gabata ce aka dira a filin Idi, inda aka fara ruguje kantinan da ke cikin fili idin kafin wayewar gari aikin gama ya gama.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Wasu na ganin wannan aiki na rusau ya zama babbar barazana ga ‘yan kasuwa da kuma wadanda suka amfana da wasu filayen da gwamnatin baya ta rabar, duk da cewa wannan aiki bai zo wa Kanawa da mamaki ba, domin tun kafin rantsar da Gwamna Abba aka ji yana bayar da sanarwar jan kunne ga duk wanda ke cikin rukunin wuraren da suka shata wa layin rushe su idan suka hau mulki, kamar gine-ginen da aka yi a harabar wasu masallatan Juma’a da na idi, kasuwanni, asibitoci, makarantu, makabartu da ganuwar da ta zagaye birnin Kano.

A ra’ayin wasu, wannan irin aiki ba zai haifar wa Gwamnatin Kwankwasiyya da mai ido ba, musamman ta yadda ake huce haushin kaza kan dami.

Wasu da suka zanta da LEADERSHI Hausa, sun bayyana cewa wannan ba shi ne Kanawa suka zabi Gwamnatin Abba kansa ba, domin mutunen da wannan rusau ya shafa sun yi asarar miliyoyin kudade.

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya bai wa Gwamnatin Abba shawarar cewa ba haka ya kamata gwamnati ta yi ba, domin kamata ya yi a samar da wani ingantaccen kwamiti ko neman shawarar masana kan yadda ya kamata a fuskanci ire-iren wadannan wurare da ake zargin an raba su ba bisa ka’ida ba.

Ya ce, “Gaggawa aikin shaidan ne, saboda haka akwai bukatar nutsuwa, sannan a yi kokarin duba maslahar al’umma ba yin fushi da fushin wasu ba.”

Wani daga cikin masu rumfuna a masallacin idi, Alhaji Abdurrahaman Yahaya ya bayyana cewa sun kwana cikin mummunan tashin hankali.

Ganau sun tabbatar da yadda aka jibge motocin ruguzau har guda uku a harabar filin idin, yayin da a gefe guda kuma wasu dandazon matasa dauke da kayan aiki ke ta kai wa wasu runfunar farmaki domin kwasar ganima ta hanyar karya kofofin rumfunan da diga.

Yanzu haka dai cikin galibin masu gine-gine a wuraren da za a ruguza ya duri ruwa a kwaryar birnin na Kano, bisa fargarbar yunkurin matasa wadanda ke amfani da wannan dama suna wasoson kayan jama’a, duk da cewa jami’an tsaro na yin bakin kokari, amma dai tun da ita gwamnati take tsaka da wannan aiki nata, hakan ke bai wa matasan karfin guiwar cewa suna lale marhabin da wannan aiki.

Babban koken da al’umma ke yi shi ne, ganin kaso 80 na wadannan gine-gine ba wadanda ake zargi da raba su ne a ciki ba, mafi yawa haya ake a ciki, mutane na ganin cewa ya kamata a bai wa mutane wa’adi domin su samu damar kwashe kayansu kafin a ruguza duk wani gini. Suna ganin cewa ya kamata gwamanati ta ayyana kwace ginin baki daya ta kuma killace shi zuwa lokacin da za ta yanke shawarar abin da ya dace a yi da su, hakan bai samu ba sai gwamnatin ta afka wa ire-iren wadannan wurare cikin dare tare da rakiyar jami’an tsaro.

Yanzu haka akwai wuraren da ake dakon isowar jirgin aikin na Gwamna Abba domin rushewa, misali akwai manyan gidajen mai da ke zagaye da Badala, musamman kan titin zuwa BUK da sauran wuraren da ke jikin makarantu, asibitoci da makabartu, wadanda su ma Gwamna Abba ya sha alwashin dirar masu nan ba da jimawa ba.

Masu sharhin al’amura na ganin rashin alfanun wannan aiki ya fi alfanunsa yawa, musamman idan aka kalli yadda wasu matasa ke amfani da wannan dama suna afka wa dukiyoyin jama’a, sannan kuma jama’a na tsoron kar irin wannan aiki ya zama na ramuwar gayya ta yadda zai zama duk wanda aka sabawa idan ya samu dama irin wannan sai ya yi amfani da ita wajen huce haushi.

Duk da cewa an samu rabuwar kai a kan matakin da gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta dauka na rushe wasu gine-gine da tsohuwar gwamnati ta siyar da filaye. Wasu suna ganin akwai amfani a kan matakin da gwamnan ya dauka, saboda a cewar wasu masu sharhi, gwamnan ya yi nazari sosai kafin daukar wannan mataki, sannan akwai dalilai ko kuma amfanin rushe-rushen kamar yadda suka zayyano.

Nan gaba duk wanda zai sa yi kadarar gwamnati zai tsaya ya tabbatar an bi ka’ida wajen siyar masa, saboda ka da wata gwamnatin ta zo ta kwace ko kuma ta ruguje.

Sannan wannan ruguje-rugujen zai yi maganin matsalolin da ake shiga a gari kamar ambaliyar ruwa idan an siyar da magudanan ruwa.

Zai taimaka wajen ilimintar da al’umma su daina zuba ido gwamnati tana siyar da hakkokinsu a mallaka wa wasu daban.

Har ila yau, zai taimaka wajen ajiye komai a kan gurbinsa, domin gwamnatoci masu zuwa nan gaba za su ji tsoron yin gini a inda bai kamata ba.

Bugu da kari, gwamnatocin da za su zo a gaba za su ji tsoron siyar da wani waje ko bayarwa ga wani mutum daya ko wasu mutane ba tare da bin ka’ida ba ko kuma ta hanyar son zuciya.

Sannan jama’ar gari za su san hakkokinsu, kuma za su ci gaba da sanya ido a kan duk wani waje da gwamnati za ta yanka da sunan fili ko kuma wani waje da gwamnati za ta sayar da sunan samar da hanyar kudin shiga ta hanyar kasuwancin hadin gwiwa tsakanin ‘yan kasuwa da gwamnati.

Kanawa
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Kanawa
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Ma’aunin Farashin Samar Da Kayayyaki Wato PPI Na Kasar Sin Ya Ragu Da Kashi 4.6 Cikin Dari A Watan Mayu

Ma’aunin Farashin Samar Da Kayayyaki Wato PPI Na Kasar Sin Ya Ragu Da Kashi 4.6 Cikin Dari A Watan Mayu

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.