ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

by Abdullahi Muh'd Sheka and Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kanawa

Tun bayan karbar rantsuwar Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin zababben gwamna Jihar Kano ya fara aiwatar da abubuwan da ya alkawarta wa Kanawa, musamman kan gine-ginen da gwamnatin jihar karkashin Abdullahi Umar Ganduje ta gina.

Domin nuna wa Kanawa da gaske gwamnatin NNPP take tun bayan rantsar da shi, gwamnan ya fara dirar mikiya a filin sukuwa da ke unguwar masu hannu da shuni ta Nasarawa, inda Gwamna Abba ya kaddamar da rushe wasu rukunin kantuna guda 90 da ake zargin na dan Gwamna Ganduje ne.

  • Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana 12 Ga Watan Yuni, Ranar Hutu

Daga nan ne kuma ya dira a tsohon otal din Daula, wanda Gwamnatin Abba ta zargi Ganduje da yin watandar filin, sai kuma tsohon gidan Jaridar Triump wanda aka tsara mayar da shi wurin kasuwar masu canjin kudaden kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Ita ma kasuwar masaukin alhazai ta gamu da sabon matakin gwamnatin, inda nan ma aka tabbatar da tarwatsa wuraren da aka rabar wa wasu masu kwalli a ido kamar yadda sabuwar gwamnatin ta ce.

Cikin daren Lahadin da ta gabata ce aka dira a filin Idi, inda aka fara ruguje kantinan da ke cikin fili idin kafin wayewar gari aikin gama ya gama.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Wasu na ganin wannan aiki na rusau ya zama babbar barazana ga ‘yan kasuwa da kuma wadanda suka amfana da wasu filayen da gwamnatin baya ta rabar, duk da cewa wannan aiki bai zo wa Kanawa da mamaki ba, domin tun kafin rantsar da Gwamna Abba aka ji yana bayar da sanarwar jan kunne ga duk wanda ke cikin rukunin wuraren da suka shata wa layin rushe su idan suka hau mulki, kamar gine-ginen da aka yi a harabar wasu masallatan Juma’a da na idi, kasuwanni, asibitoci, makarantu, makabartu da ganuwar da ta zagaye birnin Kano.

A ra’ayin wasu, wannan irin aiki ba zai haifar wa Gwamnatin Kwankwasiyya da mai ido ba, musamman ta yadda ake huce haushin kaza kan dami.

Wasu da suka zanta da LEADERSHI Hausa, sun bayyana cewa wannan ba shi ne Kanawa suka zabi Gwamnatin Abba kansa ba, domin mutunen da wannan rusau ya shafa sun yi asarar miliyoyin kudade.

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya bai wa Gwamnatin Abba shawarar cewa ba haka ya kamata gwamnati ta yi ba, domin kamata ya yi a samar da wani ingantaccen kwamiti ko neman shawarar masana kan yadda ya kamata a fuskanci ire-iren wadannan wurare da ake zargin an raba su ba bisa ka’ida ba.

Ya ce, “Gaggawa aikin shaidan ne, saboda haka akwai bukatar nutsuwa, sannan a yi kokarin duba maslahar al’umma ba yin fushi da fushin wasu ba.”

Wani daga cikin masu rumfuna a masallacin idi, Alhaji Abdurrahaman Yahaya ya bayyana cewa sun kwana cikin mummunan tashin hankali.

Ganau sun tabbatar da yadda aka jibge motocin ruguzau har guda uku a harabar filin idin, yayin da a gefe guda kuma wasu dandazon matasa dauke da kayan aiki ke ta kai wa wasu runfunar farmaki domin kwasar ganima ta hanyar karya kofofin rumfunan da diga.

Yanzu haka dai cikin galibin masu gine-gine a wuraren da za a ruguza ya duri ruwa a kwaryar birnin na Kano, bisa fargarbar yunkurin matasa wadanda ke amfani da wannan dama suna wasoson kayan jama’a, duk da cewa jami’an tsaro na yin bakin kokari, amma dai tun da ita gwamnati take tsaka da wannan aiki nata, hakan ke bai wa matasan karfin guiwar cewa suna lale marhabin da wannan aiki.

Babban koken da al’umma ke yi shi ne, ganin kaso 80 na wadannan gine-gine ba wadanda ake zargi da raba su ne a ciki ba, mafi yawa haya ake a ciki, mutane na ganin cewa ya kamata a bai wa mutane wa’adi domin su samu damar kwashe kayansu kafin a ruguza duk wani gini. Suna ganin cewa ya kamata gwamanati ta ayyana kwace ginin baki daya ta kuma killace shi zuwa lokacin da za ta yanke shawarar abin da ya dace a yi da su, hakan bai samu ba sai gwamnatin ta afka wa ire-iren wadannan wurare cikin dare tare da rakiyar jami’an tsaro.

Yanzu haka akwai wuraren da ake dakon isowar jirgin aikin na Gwamna Abba domin rushewa, misali akwai manyan gidajen mai da ke zagaye da Badala, musamman kan titin zuwa BUK da sauran wuraren da ke jikin makarantu, asibitoci da makabartu, wadanda su ma Gwamna Abba ya sha alwashin dirar masu nan ba da jimawa ba.

Masu sharhin al’amura na ganin rashin alfanun wannan aiki ya fi alfanunsa yawa, musamman idan aka kalli yadda wasu matasa ke amfani da wannan dama suna afka wa dukiyoyin jama’a, sannan kuma jama’a na tsoron kar irin wannan aiki ya zama na ramuwar gayya ta yadda zai zama duk wanda aka sabawa idan ya samu dama irin wannan sai ya yi amfani da ita wajen huce haushi.

Duk da cewa an samu rabuwar kai a kan matakin da gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta dauka na rushe wasu gine-gine da tsohuwar gwamnati ta siyar da filaye. Wasu suna ganin akwai amfani a kan matakin da gwamnan ya dauka, saboda a cewar wasu masu sharhi, gwamnan ya yi nazari sosai kafin daukar wannan mataki, sannan akwai dalilai ko kuma amfanin rushe-rushen kamar yadda suka zayyano.

Nan gaba duk wanda zai sa yi kadarar gwamnati zai tsaya ya tabbatar an bi ka’ida wajen siyar masa, saboda ka da wata gwamnatin ta zo ta kwace ko kuma ta ruguje.

Sannan wannan ruguje-rugujen zai yi maganin matsalolin da ake shiga a gari kamar ambaliyar ruwa idan an siyar da magudanan ruwa.

Zai taimaka wajen ilimintar da al’umma su daina zuba ido gwamnati tana siyar da hakkokinsu a mallaka wa wasu daban.

Har ila yau, zai taimaka wajen ajiye komai a kan gurbinsa, domin gwamnatoci masu zuwa nan gaba za su ji tsoron yin gini a inda bai kamata ba.

Bugu da kari, gwamnatocin da za su zo a gaba za su ji tsoron siyar da wani waje ko bayarwa ga wani mutum daya ko wasu mutane ba tare da bin ka’ida ba ko kuma ta hanyar son zuciya.

Sannan jama’ar gari za su san hakkokinsu, kuma za su ci gaba da sanya ido a kan duk wani waje da gwamnati za ta yanka da sunan fili ko kuma wani waje da gwamnati za ta sayar da sunan samar da hanyar kudin shiga ta hanyar kasuwancin hadin gwiwa tsakanin ‘yan kasuwa da gwamnati.

Kanawa
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Kanawa
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ma’aunin Farashin Samar Da Kayayyaki Wato PPI Na Kasar Sin Ya Ragu Da Kashi 4.6 Cikin Dari A Watan Mayu

Ma’aunin Farashin Samar Da Kayayyaki Wato PPI Na Kasar Sin Ya Ragu Da Kashi 4.6 Cikin Dari A Watan Mayu

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.