Rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi ta kama wata matar aure ‘yar shekara 19, Aisha Musa, bisa zargin yunƙurin kisan kai ta hanyar sanya guba a cikin abincin mijinta a ƙauyen Gwamma da ke ƙaramar hukumar Bauchi.
Rundunar, a cikin wata sanarwa da kakakinta, SP Nafiu Habib, a jiya, ta ce lamarin ya faru ne a ranar 12 ga Agusta, 2026.A cewar sanarwar, wacce ake zargin ta kwashe kwanaki 40 da yin aure, ta zuba wani abu da ake zargin guba ne a cikin abincin mijinta da nufin hallaka shi.
‘Yansandan sun ce wata mata ce ta kira su domin sanar da su faruwar lamarin cikin gaggawa. Nafiu ya ce, “Bayan samun rahoton, jami’an ‘C’ Division, Tafawa Balewa Estate, sun gaggauta tura jami’ai domin zuwa wurin da lamarin ya faru.
“Nan take aka ɗauki mijin zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi, inda yake ci gaba da samun kulawar likitoci kuma yana samun sauƙi sosai.”Rundunar ta ƙara da cewa an kama wacce ake zargin nan take, kuma a yayin gudanar da bincike, ta yi iƙirarin amincewa da aikata laifin da ake zarginta a kai.
Haka kuma, rundunar ta ce an samu wata kwalbar da ake zargin an taɓa ajiye guba a cikinta, tare da ragowar abincin da mijin ya ci waɗanda aka adana a matsayin hujjoji.Kwamishinan ‘yansandan andan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a tura lamarin zuwa sashen binciken manyan laifuka (SCID) na rundunar domin faɗaɗa gudanar da cikakken bincike.

Rundunar ta ce za a gurfanar da waccd ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.Rundunar ‘yansandan ta sake jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a, da kuma tabbatar da zaman lafiya da bin doka da oda a fadin jihar.Ta kuma yi kira ga jama’a da su kasance masu taka-tsan-tsan tare da gaggauta kai rahoton duk wani abu da suke zargi zuwa ofishin ‘yansanda mafi kusa.














