Biyo bayan asarar da wasu manoma a fadin kasar nan suka tabka a kakar noman bara, da fuskantar tsadar kayan noma da kuma kalubalen rashin tsaro, wani kwararre a fannin tattalin arziki da ke Jihar Kaduna, Alhaji Sabi’u Sani Sama’ila, ya shawarci manoman da suka fuskanci wadannan matsaloli, musamman kananan manoma, da kada su yi watsi da fannin na noma.
Sama’ila, ya bayar da wannan shawara ce, a hirarsa da manema labarai a Kaduna, inda ya shawarci manoman, maimakon su yi watsi da fannin, su zuba kudaden da suka tsara za su yi amfani da su wajen noman bana, a fannin kamar kiwon kifi, kajin gidan gona, kiwon zuma da kuma sauran fannonin na kiwo.
A cewarsa, bai kamata su yi watsi da fannin ba, musamman duba da cewa; su ma wadannan fannonin na kiwo, za su iya samar masu da kudaden shiga kamar yadda ya bayar da shawarar a hirarsa da manema labarai a Kaduna.
Haka zalika, ya yi nuni da cewa; a duk wata sana’a a fadin duniya, ba wai aikin noma kadai ba, dole ne mutum ya kwana da sanin cewa, yau kana iya samun riba ko kuma mai sana’ar ya yi asara. Sai dai, Sama’ila ya kuma yi kira ga gwamnati, da ta samarwa da manoma kayan aikin noma a cikin rahusa tare da kuma samar da cikakken tsaro domin manoman kasar, musamman wadanda ke Arewacin kasar, su koma gonakinsu, su ci gaba da yin noma.
Sama’ila, wanda kuma manomi ne, ya bukaci gwamnatin tarayyaidan, idan za ta raba wa manoman kayan aikin noma, ta rika raba musu a kan lokaci, musamman ma takin zamani.
Ya kuma yi kira ga daukacin matasan da ke fadin kasar nan, da su rungumi aikin noma, mai makon jiran samun aikin yi daga wurin gwamnati.
Ya kara da cewa, ta hanyar rungumar aikin noma ko kiwo, hakan zai ba su damar inganta rayuwarsu da kuma zamowa masu dogaro tare da tsayawa da kafafunsu.















Discussion about this post